An gudanar da taron karawa juna sani na shekarar 2026, na kungiyar nazarin ilmin dokokin kasashen duniya ta kasar Sin a birnin Shanghai na kasar Sin tsakanin ranakun 24 zuwa 26 ga watan nan na Afirilu.
Kuma babban taken taron na bana shi ne “Tsayawa tsayin daka wajen kare dokokin kasa da kasa, don kyautata aikin gudanar da harkokin kasashen duniya”.
Kana an gudanar da taron tattaunawa game da yadda za a kare tsarin kasa da kasa bayan Yakin Duniya Na Biyu bisa madaidaicin ra’ayin dokar kasa da kasa.
Yayin taron, shugaban sashen tanade-tanade, da ka’idoji na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Qi Dahai ya bayyana cewa, a lokacin da ake fuskantar sauye-sauyen yanayin duniya, ya kamata a tsaya tsayin daka wajen kiyaye tsarin kasashen duniya na MDD, da manufar kasashen duniya bisa dokar kasa da kasa, da ka’idar kiyaye dangantakar dake tsakanin kasashen duniya bisa kundin tsarin mulkin MDD.
Kazalika, a nasa tsokacin, mamban kwamitin dokar kasa da kasa na MDD Ma Xinmin ya ce, bisa tushen kare manufofi da ka’idojin kundin tsarin mulkin MDD, za a inganta halartar kasashe masu tasowa cikin harkokin kirkire-kirkire masu nasaba da ra’ayoyi, da manufofi, da ka’idojin dokar kasa da kasa.
Bugu da kari a yayin taron, kungiyar nazarin ilmin dokar kasashen duniya ta kasar Sin, ta fitar da sanarwa ga kasashen duniya wadda ke kiransu da su bi dokar kasa da kasa, da kaucewa amfani da matakan soja ba bisa doka ba.
Ta kuma yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su bi dokar kasa da kasa, da aiwatar da tsarin kare zaman lafiyar duniya, tare da warware sabanin dake tsakanin kasa da kasa cikin lumana.
Haka kuma, ta yi kira ga kasashen duniya da su kauracewa daukar matakan soja ba bisa doka ba, yayin raya dangantakar dake tsakanin kasashen duniya, da kare zaman lafiya da tsaron duniya, ta yadda za a inganta dunkulewar dukkanin bil Adama a nan duniya. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post