A yau Litinin 27 ga watan nan ne kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jarida, game da batutuwan da suka shafi dokar “Gaggauta Saurin Bunkasa Masana’antu” da Tarayyar Turai wato EU ta gabatar, inda ya bayyana cewa, a ranar 24 ga watan Afrilun nan, ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta mika sakamakon shawararta game da wannan doka ga hukumar EU a hukumance, inda ta bayyana matsayinta a hukumance da kuma tsananin damuwarta.
Jami’in ya ce, bangaren Sin yana ganin cewa, dokar ta sanya takunkumai da yawa kan jarin kasashen waje a sabbin manyan masana’antu masu tasowa guda hudu: wato batir, da motoci masu aiki da lantarki da karfin hasken rana, da muhimman albarkatun kasa, sannan ta sanya sharuddan bambance kayayyaki na “asalin EU” a cikin manufofin gwamnati na sayayya da ba da tallafi, wanda hakan ya zama babban shinge ga zuba jari da kuma nuna wariya a tsarin.
Kakakin ya ce, bangaren Sin zai sanya ido sosai kan abubuwan dake shafar wannan doka, kuma yana son tattaunawa da bangaren EU game da hakan.
To sai dai kuma idan bangaren EU ya yi watsi da shawarwarin bangaren Sin, ya dage sai ya zartar da wannan doka, wanda hakan zai cutar da muradun kamfanonin bangaren Sin, to Sin za ta mayar da martani yadda ya kamata, kuma da kakkarfan yanayi na kare hakkin kamfanonin kasar bisa doka. (Amina Xu)















Discussion about this post