A jiya Laraba 15 ga watan nan na Afirilu ne aka kaddamar da kalankuwar fina-finai ta babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin CMG, a birnin Ningbo na lardin Zhejiang.
Sakamakon binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN, da jami’ar Renmin ta Sin da cibiyar nazarin harkokin yayatawa tsakanin kasa suka gudanar cikin hadin gwiwa, ya tattara ra’ayoyin mutane 12,302 daga kasashen duniya 41, ya kuma nuna yadda fina-finai ko Sinima na Sin suka zamo muhimmiyar kafa ta fahimtar kasar Sin.
Da aka tambayi masu bayyana ra’ayin, dangane da hanyoyin da suke kan gaba wajen samun bayanai da suka shafi al’adun Sin, sun ce fina-finai da shirye-shiryen talabijin su ne na biyu, bayan kafafen sada zumunta dake kan gaba.
A bangaren fahimtar al’adun kasar Sin, kallon fina-finan Sin da shirye-shiryen talabijin su ne na uku, sai kuma ziyartar kasar Sin da dandana nau’o’in abincin kasar dake matsayi na farko da na biyu.Bugu da kari, kaso 81.6 bisa dari na masu bayyana ra’ayin sun bayyana yadda salon Sin na samar da tasiri mai sauki, da tasirin al’adun kasar suke kara bunkasa cikin sauri.
Har ila yau, kaso 78.6 bisa dari na masu bayyana ra’ayin sun amince cewa al’adun kasar Sin na da matukar karbuwa. Yayin da kaso 82.2 bisa dari suka nuna yadda fahimtar al’adun gargajiya na Sin ke samar da damar kara fahimtar Sin, kana kaso 77 bisa dari na masu bayyana ra’ayin ke ganin fahimtar sanannun al’adun kasar Sin na taimakawa wajen kara fahimtar kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post