Rikicin shugabanci ya ɓarke a jam’iyyar ADC reshen jihar Zamfara, inda ɓangarori biyu ke iƙirarin mallakar shugabancin jam’iyyar. Lamarin ya samo asali ne yayin da aka gudanar da taron mazabu da kuma ayyana sabon kwamiti na shugabanci.
Wani ɓangare da Malam Mohammed Mainasara ke jagoranta ya bayyana cewa shugabancin jam’iyyar na ƙasa ne ya umarce su da su kula da gudanar da taron mazaɓar jam’iyyar a Zamfara. Ya ce an naɗa shi shugaban kwamitin taron, tare da Ambasada Zubairu Yalwa a matsayin sakatare da sauran mambobi, inda ya ce sun je jihar domin tabbatar da gudanar da aikin cikin lumana.
Mainasara ya kuma bayyana cewa an cimma matsayar kafa sabon kwamitin zartarwa na jiha (EXCO) ta hanyar sulhu da amincewar masu ruwa da tsaki. A cewarsa, an zabi Malam Shehu Gulubba a matsayin shugaban jam’iyya na jihar, yayin da Dr. Ahmad Hashim ya zama sakatare, tare da Jafar Aliyu a matsayin shugaban matasa da Maryam Abdullahi a matsayin shugabar mata.
A nasa ɓangaren, sabon shugaban da aka ce an zaɓa, Malam Shehu Maishanu, ya yi alƙawarin yin aiki tukuru wajen ƙarfafa jam’iyyar da tabbatar da nasararta a faɗin jihar Zamfara. Ya ce jagorancinsu zai mayar da hankali kan ci gaban al’umma da kuma tabbatar da haɗin kai a cikin jam’iyyar.
Sai dai wani ɓangare ƙarƙashin jagorancin Kabiru Garba Gusau ya yi watsi da sakamakon taron, yana mai cewa shi ne halastaccen shugaban jam’iyyar a jihar. Ya zargi wasu da haɗa kai domin tayar da zaune tsaye, tare da gargaɗin cewa ba za su amince da abin da ya faru ba, inda ya ce sun riga sun kai rahoto ga ‘yansanda da DSS. Ya kuma bayyana cewa ya dakatar da duk waɗanda suka halarci taron, yana mai cewa yana da ikon kundin tsarin jam’iyya na yin hakan.















Discussion about this post