ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuskuren Furuci Daga Christopher Musa

by Sulaiman
1 month ago
Sojoji

Ministan tsaro, Christopher Musa, ya sake faɗawa wata matsala. A watan Oktoba, 2024, Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya sallame shi daga matsayin shugaban tsaro na Nijeriya bayan wasu rahotannin sun bayyana na yunƙurin juyin mulki da wasu fusatattun jami’an soji suka yi.

Kuma a wani labarin na daban, Musa, tare da shugabannin tsaro da suka haɗa da shugaban sojojin ruwa da na sama an kore su, yayin da an kama wasu jami’an sojoji sakamakon ƙorafe-ƙorafe game da rashin isasshen kuɗi ga sojoji.

A farkon wannan wata, ministan tsaro, a cikin wata hira a talabijin, ya ce gwamnati ta ɗaga mafi ƙarancin albashin sojojin Nijeriya daga naira 49,000 zuwa naira 100,000.

ADVERTISEMENT

Tsohon shugaban ma’aikatan tsaro, Lucky Irabor da tsohon shugaban sojoji, Tukur Buratai suna da daman faɗin haka a lokacin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, amma ba su taɓa yin buƙatar sake duban albashin ƴan sojoji ba, waɗanda a cewar rahotanni na baya-bayan nan suna ɗaya daga cikin mafi ƙarancin albashi a Afirka.

Amma gazawar ba nasu janar ba ne kawai, Abayomi Olonisakan, Lucky Irabor, Tukur Buratai da Farouk Yahaya. Haka kuma gazawa ce ta manufofi da rashin jagorancin siyasa daga gwamnatin baya.Ba shi da wata gaskiyar hangen nesa na sauya sojojin ƙasa zuwa rundunar tsaro mai amfani da fasaha da ta dace da ƙarni na 21, kuma cire siyan kayan aiki da kwasa-kwasai na manyan sojoji, shugabancin siyasa ba shi da wata manufa game da yadda za a kashe kuɗaɗen sojoji.

LABARAI MASU NASABA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

Amma tambayar ita ce, shin maganar Musa kuskuren furuci ce ko kuwa yunƙurin da ya tsara na tattauna batun tsaro na ƙasa da siyasa wanda ba za a iya gabatar wa shugaban ƙasa da kansa ba tare da martani mai ƙarfi ba?Ko ta wata hanya ga wanda ya rasa matsayin shugaban tsaro saboda shiga tsaka mai wuya a tsakanin manyan jami’an soji, minista ya nuna jarumta wajen kawo batun rashin jin daɗin jami’ai a ƙarƙashin rundunar.

A cikin kwanakin baya, ministan ya fito bayyanar jama’a ya musanta cewa baya shirya yin murabus, bayan ganawa da shugaban ƙasa a sirrance.Maganar cewa Musa ya yi murabus kawai jita-jita ne kuma bai san ko wane ne ke bayan hakan ba, har yanzu Musa ba zai iya kauce wa saƙon da ke cikin bayaninsa na baya da kuma iƙirarin murabus ɗinsa ba.

Saƙo ne na talauci mai tsanani a cikin rundunar sojoji, wanda ba za a iya ware shi daga rashin tsaro da ke addabar sassar ƙasar ba. Duk da babu rahotanni kan abin da shugaban ƙasa da minista suka tattauna a sirrince, amma tattaunawar ta gudana ba tare da manyan jami’an soji ba kuma a tsakiyar jita-jita, yana nuna cewa akwai wani lamari na gaggawa.

Rundunar sojojin Nijeriya a wani lokaci ita ce cibiyar da tafi kowa aiki da ladabi a ƙasar. Amma a yau, sabbin ɗauka a rundunar sojojin Nijerya kamar suna biyan kuɗin kaki da kansu.

Sojojin da aka jibge a kan manyan hanyoyi a yankunan da kef ama da rashin tsaro suna ƙara ɗaukar dabi’un ƴansanda. Tsoron da ake yi shi ne samun rugujewar ladabi da ƙwarin gwiwa a rundunar soji zai yi tasiri a duk cikin al’umma.

A mataki mai ɗorewa, watakila Nijeriya ba za ta jure irin wannan gurɓacewar ga sojoji ba. Amma a ƙarshe, duk alhakki yana tsayawa ne a tebur ɗaya kawai.

Musa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang
  • Sulaiman
    Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris
  • Sulaiman
    Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu
  • Sulaiman
    Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

MASU ALAKA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya
Labarai

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Labarai

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Musa
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Next Post
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Jinping Mai Taken “Hanzarta Gina Sin Mai Koshin Lafiya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Muhimmiyar Makalar Xi Jinping Mai Taken "Hanzarta Gina Sin Mai Koshin Lafiya"

LABARAI MASU NASABA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Musa

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Musa

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Musa

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.