A fitowarta ta ranar 1 ga watan Agusta, mujallar “Qiushi” za ta wallafa wata muhimmiyar makala da shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya rubuta mai taken “Hanzarta Gina Sin Mai Koshin Lafiya”.
Makalar ta jaddada cewa, gina kasar Sin mai koshin lafiya nan da shekarar 2035 wani kwakkwaran mataki ne bisa manyan tsare-tsare da gwamnatin kasar ta dauka. Shirin bunkasa ci gaban kasa da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15 wani lokaci ne mai muhimmanci ga cimma wannan buri, kuma ya zama wajibi a tsara cikakkun shirye-shirye, tare da kara azamar ganin an samu gagarumin ci gaba mai ma’ana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














