Ƙungiyar Kwankwasiyya ta ƙaryata rahotannin da ke cewa jagoranta, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin ficewa daga jam’iyyar NDC.
Rahotannin sun biyo bayan labarin cewa jam’iyyar ta maye gurbin wasu ‘yan takarar da ƙungiyar ta gabatar a Jihar Kano.
Da yake magana kan lamarin, kakakin Kwankwasiyya, Dokta Habib Sale, ya ce babu wata tattaunawa ko shawara da aka yanke kan batun ficewar Kwankwaso daga jam’iyyar.
Ya bayyana rahotannin a matsayin jita-jita da ake yaɗawa a kafafen yaɗa labarai da kuma shafukan sada zumunta.
“Shugabanmu bai taɓa tattaunawa da kowa kan ficewa daga jam’iyyar ba. Mu ma mun ga labarin ne kamar kowa,” in ji Sale.
Ya kuma bayyana cewa an zaɓi ‘yan takarar da Kwankwasiyya ta goyi baya ne ta hanyar zaɓen fidda-gwani da aka gudanar a ranar 29 ga watan Mayu, kuma an bi dukkanin matakai ba tare da wata matsala ba a lokacin.
A cewarsa, an miƙa jerin sunayen ‘yan takara bayan kammala zaɓen, kuma duk wani mataki da za a ɗauka yanzu yana hannun jam’iyya bisa ƙa’idojinta.
Wannan bayani ya biyo bayan rahotannin da ke cewa NDC ta sauya wasu ‘yan takarar da Kwankwasiyya ta gabatar a Kano, sakamakon saɓani kan yarjejeniyar raba muƙamai tsakanin ɓangarorin biyu.
Rahoton ya nuna cewa an ware kashi 60 cikin 100 na muƙamai ga Kwankwasiyya, yayin da kashi 40 cikin 100 kuma aka bai wa ɓangaren jam’iyyar na asali.
Duk da wannan rikici, Kwankwasiyya na ci gaba da cewa ba a yanke wani hukunci ba kan makomar dangantakarta da jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.














Discussion about this post