ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

by Sadiq
28 minutes ago

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta ƙaryata rahotannin da ke cewa jagoranta, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin ficewa daga jam’iyyar NDC.

Rahotannin sun biyo bayan labarin cewa jam’iyyar ta maye gurbin wasu ‘yan takarar da ƙungiyar ta gabatar a Jihar Kano.

Da yake magana kan lamarin, kakakin Kwankwasiyya, Dokta Habib Sale, ya ce babu wata tattaunawa ko shawara da aka yanke kan batun ficewar Kwankwaso daga jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana rahotannin a matsayin jita-jita da ake yaɗawa a kafafen yaɗa labarai da kuma shafukan sada zumunta.

“Shugabanmu bai taɓa tattaunawa da kowa kan ficewa daga jam’iyyar ba. Mu ma mun ga labarin ne kamar kowa,” in ji Sale.

LABARAI MASU NASABA

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

Ya kuma bayyana cewa an zaɓi ‘yan takarar da Kwankwasiyya ta goyi baya ne ta hanyar zaɓen fidda-gwani da aka gudanar a ranar 29 ga watan Mayu, kuma an bi dukkanin matakai ba tare da wata matsala ba a lokacin.

A cewarsa, an miƙa jerin sunayen ‘yan takara bayan kammala zaɓen, kuma duk wani mataki da za a ɗauka yanzu yana hannun jam’iyya bisa ƙa’idojinta.

Wannan bayani ya biyo bayan rahotannin da ke cewa NDC ta sauya wasu ‘yan takarar da Kwankwasiyya ta gabatar a Kano, sakamakon saɓani kan yarjejeniyar raba muƙamai tsakanin ɓangarorin biyu.

Rahoton ya nuna cewa an ware kashi 60 cikin 100 na muƙamai ga Kwankwasiyya, yayin da kashi 40 cikin 100 kuma aka bai wa ɓangaren jam’iyyar na asali.

Duk da wannan rikici, Kwankwasiyya na ci gaba da cewa ba a yanke wani hukunci ba kan makomar dangantakarta da jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

MASU ALAKA

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir
Manyan Labarai

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima
Manyan Labarai

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026
Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.