Rundunonin sojin Sin da Afrika ta Kudu sun cimma matsaya kan ci gaba da zurfafa hadin gwiwa mai karfi ta kowace fuska.
Kakakin ma’aikatar tsaron Sin Zhang Xiaogang ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai a yau Talata, inda ya kara da cewa, ministan tsaron kasar Sin Dong Jun da ministan tsaro da kula da harkokin mazan jiya na Afrika ta Kudu ne suka cimma matsayar yayin ziyarar da Dong Jun din ya kai Afrika ta Kudu bisa gayyatarsa da aka yi.
Karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, rundunonin sojin kasashen za su ci gaba da tuntubar juna da inganta tsare-tsaren hadin gwiwa da musaya a bangarori na musamman da zurfafa bayar da ilimi da horo, domin zama misalin hadin gwiwar soji tsakanin kasashe masu tasowa. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post