Amurka ta sake cusa matsalolinta ga wasu.
Bisa rahotannin da aka bayar, an ce, gwamnatin Amurka na shirin gina wurin kula da marasa lafiya mai gadaje 50 a sansanin sojin sama na Laikipia dake kasar Kenya, domin a ajiye ‘yan Amurkan da ke cikin hadarin kamuwa da cutar Ebola, maimakon mayar da su Amurka kamar yadda aka saba. Har ma sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya fadi karara cewa: “Ba za mu bari ko da mutum daya da ya harbu da cutar Ebola ya shiga Amurka ba.” Wato ke nan ba za a bari Amurkawa su fuskanci hadarin ba, amma al’ummar Afirka za su iya fuskantar shi.
Duk da cewa Amurka tana da mafi kyawun hanyoyin kiwon lafiya da karfin tattalin arziki, maimakon ta yi aikin da ya dace da matsayinta na kasa mai girma, sai ta nuna tsananin son kai, ta jefa matsaloli da annoba ga Afirka don neman kare kanta daga hadarin cutar. Yayin da suka fuskanci wannan rashin adalci, al’ummar Kenya ba su yi shiru ba. Babbar kotun Kenya a ranar 29 ga watan Mayu ta dakatar da wannan shiri, saboda kasancewarsa “Mai barazana ga rayuka”, kuma za ta saurari karar a gobe Talata 2 ga watan nan. Cibiyar Katiba da ta shigar da karar a madadin ‘yan Kenya, ta ce “Babban abin da ke cikin wannan shari’a shi ne tabbatar da bin tsarin mulki, da kare lafiyar jama’a, da kuma tabbatar da cewa babu wata gwamnati da za ta iya fifita son zuciya a kan rayuka da tsaron al’ummar Kenya.” Babban sakataren kungiyar likitocin Kenya, Dr. Davji Bhimji Atellah, ya fada cikin bacin rai cewa, “Ba za mu zauna kallo muna barin Kenya ta zama ‘kebabben tsibiri’ na wadannan cututtuka masu hadari ba. Abin da yake da hadari ga Amurka hadari ne ga Kenya.” Har wa yau, Lauya Miguna Miguna ya rubuta a shafinsa na sada zumunta cewa, “Kawo Amurkawa da suka yi cudanya da masu cutar Ebola zuwa Kenya, ko da wane dalili cin amanar kasa ne”. Shi ma wani mazaunin birnin Nairobi, mai suna Robert Kiberenge, ya yi tambayar cewa “Me ya sa Amurka take ganin rayukan Amurkawa sun fi na ‘yan Kenya muhimmanci, har za ta kafa wurin kula da Amurkawa a Kenya?
“Hakika, Amurka ta saba da cusa matsalolinta ga kasashen Afirka – duk lokacin da Washington ta ga wani abu mai hadari da ba za ta iya ajiyewa a cikin yankunanta ba, sai ta sami wata kasa ta Afirka da za ta mikawa. A shekarun baya, Amurka ta ci gaba da korar bakin haure, da masu laifi da ba ta son karba, inda ta rika tura su zuwa kasashen Eswatini, da Saliyo da sauran wasu kasashen Afirka. Wadannan mutane masu manyan laifuka barazana ne ga al’umma, ana sanya su a cikin kasashen Afirka masu rauni da rashin wadataccen tsarin lafiya, wanda hakan ke sa al’ummar Afirka shan wahalar matsalolin Amurka, kuma ana take hakkin kasashen na Afirka da rayukan al’ummarsu. Wannan nuna bambanci ya shaida yadda Amurka ke nuna fin karfi, da dorawa kasashen Afirka nauyin da ya wuce na su.
A yanzu, mutane sama da dubu daya ake zaton sun kamu da annobar Ebola a Jamhuriyar Demokuradiyyar Cango, cutar da tuni ta halaka sama da mutane 200, kuma nahiyar Afirka na bukatar gudummawar kasashen duniya. Babban abin da ake bukata don yakar annoba shi ne sassan kasa da kasa su hada kawunansu, su dauki nauyin tare, a maimakon jefa matsalar ga wasu. Amurka na neman kauracewa daukar nauyin da ke wuyanta, da nuna bambanci game da hakkin dan Adam, bisa yadda ta sha jefa matsalolinta ga nahiyar Afirka. Kamata ya yi sassan kasa da kasa su nuna adawa da irin wannan mataki na nuna fin karfi. Tabbas za a kai ga inganta tsaron al’ummomin duniya, muddin aka daina nuna bambanci, tare da tsayawa kan warware matsalolin da duniya ke fuskanta tare.















Discussion about this post