ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 weeks ago
Kenya

Amurka ta sake cusa matsalolinta ga wasu.

Bisa rahotannin da aka bayar, an ce, gwamnatin Amurka na shirin gina wurin kula da marasa lafiya mai gadaje 50 a sansanin sojin sama na Laikipia dake kasar Kenya, domin a ajiye ‘yan Amurkan da ke cikin hadarin kamuwa da cutar Ebola, maimakon mayar da su Amurka kamar yadda aka saba. Har ma sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya fadi karara cewa: “Ba za mu bari ko da mutum daya da ya harbu da cutar Ebola ya shiga Amurka ba.” Wato ke nan ba za a bari Amurkawa su fuskanci hadarin ba, amma al’ummar Afirka za su iya fuskantar shi.

Duk da cewa Amurka tana da mafi kyawun hanyoyin kiwon lafiya da karfin tattalin arziki, maimakon ta yi aikin da ya dace da matsayinta na kasa mai girma, sai ta nuna tsananin son kai, ta jefa matsaloli da annoba ga Afirka don neman kare kanta daga hadarin cutar. Yayin da suka fuskanci wannan rashin adalci, al’ummar Kenya ba su yi shiru ba. Babbar kotun Kenya a ranar 29 ga watan Mayu ta dakatar da wannan shiri, saboda kasancewarsa “Mai barazana ga rayuka”, kuma za ta saurari karar a gobe Talata 2 ga watan nan. Cibiyar Katiba da ta shigar da karar a madadin ‘yan Kenya, ta ce “Babban abin da ke cikin wannan shari’a shi ne tabbatar da bin tsarin mulki, da kare lafiyar jama’a, da kuma tabbatar da cewa babu wata gwamnati da za ta iya fifita son zuciya a kan rayuka da tsaron al’ummar Kenya.” Babban sakataren kungiyar likitocin Kenya, Dr. Davji Bhimji Atellah, ya fada cikin bacin rai cewa, “Ba za mu zauna kallo muna barin Kenya ta zama ‘kebabben tsibiri’ na wadannan cututtuka masu hadari ba. Abin da yake da hadari ga Amurka hadari ne ga Kenya.” Har wa yau, Lauya Miguna Miguna ya rubuta a shafinsa na sada zumunta cewa, “Kawo Amurkawa da suka yi cudanya da masu cutar Ebola zuwa Kenya, ko da wane dalili cin amanar kasa ne”. Shi ma wani mazaunin birnin Nairobi, mai suna Robert Kiberenge, ya yi tambayar cewa “Me ya sa Amurka take ganin rayukan Amurkawa sun fi na ‘yan Kenya muhimmanci, har za ta kafa wurin kula da Amurkawa a Kenya?

ADVERTISEMENT

“Hakika, Amurka ta saba da cusa matsalolinta ga kasashen Afirka – duk lokacin da Washington ta ga wani abu mai hadari da ba za ta iya ajiyewa a cikin yankunanta ba, sai ta sami wata kasa ta Afirka da za ta mikawa. A shekarun baya, Amurka ta ci gaba da korar bakin haure, da masu laifi da ba ta son karba, inda ta rika tura su zuwa kasashen Eswatini, da Saliyo da sauran wasu kasashen Afirka. Wadannan mutane masu manyan laifuka barazana ne ga al’umma, ana sanya su a cikin kasashen Afirka masu rauni da rashin wadataccen tsarin lafiya, wanda hakan ke sa al’ummar Afirka shan wahalar matsalolin Amurka, kuma ana take hakkin kasashen na Afirka da rayukan al’ummarsu. Wannan nuna bambanci ya shaida yadda Amurka ke nuna fin karfi, da dorawa kasashen Afirka nauyin da ya wuce na su.

A yanzu, mutane sama da dubu daya ake zaton sun kamu da annobar Ebola a Jamhuriyar Demokuradiyyar Cango, cutar da tuni ta halaka sama da mutane 200, kuma nahiyar Afirka na bukatar gudummawar kasashen duniya. Babban abin da ake bukata don yakar annoba shi ne sassan kasa da kasa su hada kawunansu, su dauki nauyin tare, a maimakon jefa matsalar ga wasu. Amurka na neman kauracewa daukar nauyin da ke wuyanta, da nuna bambanci game da hakkin dan Adam, bisa yadda ta sha jefa matsalolinta ga nahiyar Afirka. Kamata ya yi sassan kasa da kasa su nuna adawa da irin wannan mataki na nuna fin karfi. Tabbas za a kai ga inganta tsaron al’ummomin duniya, muddin aka daina nuna bambanci, tare da tsayawa kan warware matsalolin da duniya ke fuskanta tare.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Kenya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Kenya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.