Jami’ai da kwararru daga kasar Sin da kasashen Afirka, sun yi kira da a zurfafa hadin kai a fannin raya ababen more rayuwa, bisa jagorancin sassa masu zaman kansu ta yadda za a rage gibin karancin ababen more rayuwa a kasashen Afirka.
Mahalarta taron sun yi kiran ne a kwanan nan, a gefen taron kaddamar da taron ‘yan kasuwar Sin da Afirka, wanda ya gudana a hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU dake birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha.
Taron ya hallara wakilai na fitattun kamfanonin kasar Sin dake gudanar da hada-hada a Afirka, da jami’an kungiyar AU, da kwararru na Sin da Afirka a fannin raya ababen more rayuwa.
Cikin jawabinsa yayin taron, babban jami’in tawagar wakilci ta kasar Sin a hedkwatar AU Wang Ligui, ya yi kira da a kara saita muhimman shirye-shiryen da AU ke jagoranta, na bunkasa samar da ababen more rayuwa a Afirka da na shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ta Sin, ta yadda za a ingiza nasarar samar da karin ababen more rayuwa a nahiyar.
A nata tsokacin kuwa, shugabar sashen gudanarwa da kula da kayayyaki a hukumar gudanarwa kungiyar AU Nelisiwe Siphelele Mathabela, cewa ta yi hadin gwiwar Afirka da Sin a fannin samar da ababen more rayuwa, muhimmin bangare ne na kawancensu, wanda ke ingiza bunkasar masana’antu da raya tattalin arziki a nahiyar. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post