ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ni Yanzu Ɗan Siyasa Ne Mai Zaman Kansa, Ina Damar Alaƙa Da Kowace Jam’iyya – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 month ago

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana cewar yanzu haka shi ɗan siyasa ne mai zaman kansa wanda ke da damar alaƙa da kowace jam’iyyar siyasa a faɗin ƙasar nan domin ganin an ceto Nijeriya daga halin da ta ke ciki.

Bala, wanda ya shaida hakan a lokacin da ya amshi baƙwancinsa jigo a jam’iyyar ADC, Mista Peter Obi a gidan gwamnatin jihar Bauchi ranar Alhamis, bayan sun yi ganawar sirri, inda ya wa ‘yan jarida cewa, jam’iyyarsa ta PDP a halin yanzu tana cikin wani hali da suke zaman jiran hukuncin kotun domin sanin matsayarsu.

Don haka ya ce, a shirye yake ya hada kai da kowace jam’iyya domin ganin an ceto Nijeriya. Gwamna Bala Mohammed ya ce magance manyan ƙalubalen Najeriya na buƙatar haɗin kai.Ya bayyana cewa ganawar da suka yi da Obi ta mayar da hankali ne kan haɗin kan ƙasa da kuma aiki tare, yana mai jaddada cewa ba a gudanar da ita bisa son rai na jam’iyya ba.”Tabbas, dukkanmu muna cikin ɓangaren adawa, shi ya sa na kira wannan tattaunawa ta siyasa.

ADVERTISEMENT

Amma ba za mu bayyana muku duk abin da aka tattauna ba,” in ji shi.Ya kara da cewa tattaunawar tana da nufin neman haɗa kai domin samar da tsarin da za su tunƙari zaɓen 2027.”Dole sai da jam’iyyar siyasa za mu hada ƙarfi waje guda,” don haka ne ya ce suna ci gaba da tattauna yanayin siyasar da kuma inda za su haɗu wato jam’iyya guda da nufin ceto Nijeriya daga halin ni’yasu.

Bala Mohammed ya bayyana ziyarar Obi a matsayin wata alama ta ƙoƙarin kyautata alaka tsakanin yankuna, yana mai cewa, “Wannan ziyara ta shafi haɗin gwiwa, aiki tare, da sake gina ƙasa domin dawo da daidaiton iko da magabatanmu suka kafa, wanda daga baya aka yi watsi da shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Ya kuma lura cewa jam’iyyun adawa na duba yiwuwar ƙulla kawance na dabaru.Tun da farko, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki daga yankin Kudu maso Gabas, Arewa maso Gabas, da sauran yankuna da su haɗa kai domin sake gina Nijeriya.

Obi ya roƙi Bala da sauran masu ruwa da tsaki da su yi aiki tare domin ci gaban ƙasa da kuma ceto ta daga rugujewa.Ya bayyana cewa ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da zumunci tsakanin shugabanni daga yankuna daban-daban, musamman a Arewa maso Gabas.

“Munaso mu gina ƙasa mai haɗin kai domin makomar ‘ya’yanmu. Nijeriya ba za ta iya ci gaba da tafiya a wannan yanayin ba; muna kan hanyar da ba ta dace ba kuma dole mu gyara hakan domin amfanuwar kowannenmu” in ji shi.Ya jaddada cewa kishin ƙasa ya kamata ya fi fifiko a kan alaƙar jam’iyya, yana mai cewa matsaloli kamar rashin tsaro da tashin farashin abinci na shafar dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da jam’iyya, ƙabila ko addini ba.

“Babu wata jam’iyya da ke sa abinci ya yi araha a kasuwa. Babu wata ƙabila ko addini da ke sayen burodi a farashi mai sauƙi fiye da wasu. Abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da tsaro da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya,” ya ƙara da cewa.Obi, wanda jigo ne a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya jaddada cewa idan rashin tsaro ya afku, ko ta hanyar garkuwa da mutane ko tashin hankali, ba a bambanta waɗanda abin ya shafa da jam’iyya ko ƙabila, yana mai nuna gaggawar ɗaukar matakin gama-gari.

Obi ya je ziyarar tare da wasu fitattun ‘yan siyasa daga Kudu maso Gabas, ciki har da tsohon gwamnan Jihar Imo, Achike Udenwa, Ben Obi, Sanata Enyinnaya Abaribe, Sanata Victor Umeh, Farfesa Udenta O. Udenta, da Tanko Yunusa, da sauransu.

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.