ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ni Yanzu Ɗan Siyasa Ne Mai Zaman Kansa, Ina Damar Alaƙa Da Kowace Jam’iyya – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 months ago

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana cewar yanzu haka shi ɗan siyasa ne mai zaman kansa wanda ke da damar alaƙa da kowace jam’iyyar siyasa a faɗin ƙasar nan domin ganin an ceto Nijeriya daga halin da ta ke ciki.

Bala, wanda ya shaida hakan a lokacin da ya amshi baƙwancinsa jigo a jam’iyyar ADC, Mista Peter Obi a gidan gwamnatin jihar Bauchi ranar Alhamis, bayan sun yi ganawar sirri, inda ya wa ‘yan jarida cewa, jam’iyyarsa ta PDP a halin yanzu tana cikin wani hali da suke zaman jiran hukuncin kotun domin sanin matsayarsu.

Don haka ya ce, a shirye yake ya hada kai da kowace jam’iyya domin ganin an ceto Nijeriya. Gwamna Bala Mohammed ya ce magance manyan ƙalubalen Najeriya na buƙatar haɗin kai.Ya bayyana cewa ganawar da suka yi da Obi ta mayar da hankali ne kan haɗin kan ƙasa da kuma aiki tare, yana mai jaddada cewa ba a gudanar da ita bisa son rai na jam’iyya ba.”Tabbas, dukkanmu muna cikin ɓangaren adawa, shi ya sa na kira wannan tattaunawa ta siyasa.

ADVERTISEMENT

Amma ba za mu bayyana muku duk abin da aka tattauna ba,” in ji shi.Ya kara da cewa tattaunawar tana da nufin neman haɗa kai domin samar da tsarin da za su tunƙari zaɓen 2027.”Dole sai da jam’iyyar siyasa za mu hada ƙarfi waje guda,” don haka ne ya ce suna ci gaba da tattauna yanayin siyasar da kuma inda za su haɗu wato jam’iyya guda da nufin ceto Nijeriya daga halin ni’yasu.

Bala Mohammed ya bayyana ziyarar Obi a matsayin wata alama ta ƙoƙarin kyautata alaka tsakanin yankuna, yana mai cewa, “Wannan ziyara ta shafi haɗin gwiwa, aiki tare, da sake gina ƙasa domin dawo da daidaiton iko da magabatanmu suka kafa, wanda daga baya aka yi watsi da shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

“Ya kuma lura cewa jam’iyyun adawa na duba yiwuwar ƙulla kawance na dabaru.Tun da farko, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki daga yankin Kudu maso Gabas, Arewa maso Gabas, da sauran yankuna da su haɗa kai domin sake gina Nijeriya.

Obi ya roƙi Bala da sauran masu ruwa da tsaki da su yi aiki tare domin ci gaban ƙasa da kuma ceto ta daga rugujewa.Ya bayyana cewa ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da zumunci tsakanin shugabanni daga yankuna daban-daban, musamman a Arewa maso Gabas.

“Munaso mu gina ƙasa mai haɗin kai domin makomar ‘ya’yanmu. Nijeriya ba za ta iya ci gaba da tafiya a wannan yanayin ba; muna kan hanyar da ba ta dace ba kuma dole mu gyara hakan domin amfanuwar kowannenmu” in ji shi.Ya jaddada cewa kishin ƙasa ya kamata ya fi fifiko a kan alaƙar jam’iyya, yana mai cewa matsaloli kamar rashin tsaro da tashin farashin abinci na shafar dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da jam’iyya, ƙabila ko addini ba.

“Babu wata jam’iyya da ke sa abinci ya yi araha a kasuwa. Babu wata ƙabila ko addini da ke sayen burodi a farashi mai sauƙi fiye da wasu. Abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da tsaro da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya,” ya ƙara da cewa.Obi, wanda jigo ne a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya jaddada cewa idan rashin tsaro ya afku, ko ta hanyar garkuwa da mutane ko tashin hankali, ba a bambanta waɗanda abin ya shafa da jam’iyya ko ƙabila, yana mai nuna gaggawar ɗaukar matakin gama-gari.

Obi ya je ziyarar tare da wasu fitattun ‘yan siyasa daga Kudu maso Gabas, ciki har da tsohon gwamnan Jihar Imo, Achike Udenwa, Ben Obi, Sanata Enyinnaya Abaribe, Sanata Victor Umeh, Farfesa Udenta O. Udenta, da Tanko Yunusa, da sauransu.

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.