ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ni Yanzu Ɗan Siyasa Ne Mai Zaman Kansa, Ina Damar Alaƙa Da Kowace Jam’iyya – Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 months ago

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana cewar yanzu haka shi ɗan siyasa ne mai zaman kansa wanda ke da damar alaƙa da kowace jam’iyyar siyasa a faɗin ƙasar nan domin ganin an ceto Nijeriya daga halin da ta ke ciki.

Bala, wanda ya shaida hakan a lokacin da ya amshi baƙwancinsa jigo a jam’iyyar ADC, Mista Peter Obi a gidan gwamnatin jihar Bauchi ranar Alhamis, bayan sun yi ganawar sirri, inda ya wa ‘yan jarida cewa, jam’iyyarsa ta PDP a halin yanzu tana cikin wani hali da suke zaman jiran hukuncin kotun domin sanin matsayarsu.

Don haka ya ce, a shirye yake ya hada kai da kowace jam’iyya domin ganin an ceto Nijeriya. Gwamna Bala Mohammed ya ce magance manyan ƙalubalen Najeriya na buƙatar haɗin kai.Ya bayyana cewa ganawar da suka yi da Obi ta mayar da hankali ne kan haɗin kan ƙasa da kuma aiki tare, yana mai jaddada cewa ba a gudanar da ita bisa son rai na jam’iyya ba.”Tabbas, dukkanmu muna cikin ɓangaren adawa, shi ya sa na kira wannan tattaunawa ta siyasa.

ADVERTISEMENT

Amma ba za mu bayyana muku duk abin da aka tattauna ba,” in ji shi.Ya kara da cewa tattaunawar tana da nufin neman haɗa kai domin samar da tsarin da za su tunƙari zaɓen 2027.”Dole sai da jam’iyyar siyasa za mu hada ƙarfi waje guda,” don haka ne ya ce suna ci gaba da tattauna yanayin siyasar da kuma inda za su haɗu wato jam’iyya guda da nufin ceto Nijeriya daga halin ni’yasu.

Bala Mohammed ya bayyana ziyarar Obi a matsayin wata alama ta ƙoƙarin kyautata alaka tsakanin yankuna, yana mai cewa, “Wannan ziyara ta shafi haɗin gwiwa, aiki tare, da sake gina ƙasa domin dawo da daidaiton iko da magabatanmu suka kafa, wanda daga baya aka yi watsi da shi.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

“Ya kuma lura cewa jam’iyyun adawa na duba yiwuwar ƙulla kawance na dabaru.Tun da farko, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki daga yankin Kudu maso Gabas, Arewa maso Gabas, da sauran yankuna da su haɗa kai domin sake gina Nijeriya.

Obi ya roƙi Bala da sauran masu ruwa da tsaki da su yi aiki tare domin ci gaban ƙasa da kuma ceto ta daga rugujewa.Ya bayyana cewa ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da zumunci tsakanin shugabanni daga yankuna daban-daban, musamman a Arewa maso Gabas.

“Munaso mu gina ƙasa mai haɗin kai domin makomar ‘ya’yanmu. Nijeriya ba za ta iya ci gaba da tafiya a wannan yanayin ba; muna kan hanyar da ba ta dace ba kuma dole mu gyara hakan domin amfanuwar kowannenmu” in ji shi.Ya jaddada cewa kishin ƙasa ya kamata ya fi fifiko a kan alaƙar jam’iyya, yana mai cewa matsaloli kamar rashin tsaro da tashin farashin abinci na shafar dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da jam’iyya, ƙabila ko addini ba.

“Babu wata jam’iyya da ke sa abinci ya yi araha a kasuwa. Babu wata ƙabila ko addini da ke sayen burodi a farashi mai sauƙi fiye da wasu. Abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da tsaro da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya,” ya ƙara da cewa.Obi, wanda jigo ne a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya jaddada cewa idan rashin tsaro ya afku, ko ta hanyar garkuwa da mutane ko tashin hankali, ba a bambanta waɗanda abin ya shafa da jam’iyya ko ƙabila, yana mai nuna gaggawar ɗaukar matakin gama-gari.

Obi ya je ziyarar tare da wasu fitattun ‘yan siyasa daga Kudu maso Gabas, ciki har da tsohon gwamnan Jihar Imo, Achike Udenwa, Ben Obi, Sanata Enyinnaya Abaribe, Sanata Victor Umeh, Farfesa Udenta O. Udenta, da Tanko Yunusa, da sauransu.

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

Yadda Fasahar Mutum-Mutumin Inji Ke Kara Shiga Fannonin Rayuwa A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.