ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyawun Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
3 years ago
Alkawari

A watan Nuwambar shekarar 2021 ne aka gudanar da taro karo na 8, na ministocin kasashe mambobin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ko FOCAC, ta kafar bidiyo daga Dakar na kasar Senegal. 

Yayin taron, an amince da wasu manufofi, ciki har da yarjejeniyar Dakar. A kuma lokacin ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da kaddamar da wasu shirye shirye guda 9, na raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

  • Kwamitin Kula Da Ladabtarwa Da Sanya Ido Na Kwamitin Kolin JKS Ya Tsara Dabarun Daukar Kwararan Matakai Wajen Tafiyar Da Harkokin Jam’iyya Bisa Tsauraran Matakan Da’a

Masharhanta na kallon wannan shirye shirye a matsayin ginshikai da zai kara karfafa kawancen gargajiya tsakanin Sin da Afirka, za su kuma ingiza burin da ake da shi, na gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya a sabon zamani da muke ciki.

ADVERTISEMENT

Yanzu haka, an shafe shekara daya ko fiye tun bayan gudanar da wancan taro na ministoci. Kuma duk da cewa an samu manyan sauye-sauye a harkokin kasa da kasa, da tarin kalubale, da yanayi na rashin tabbas a wasu sassa, a daya bangaren Sin da kasashen Afirka, sun ci gaba da aiwatar da matakan goyawa juna baya, da zurfafa kyakkaywar alakar su yadda ya kamata. Kaza lika sassan biyu sun cimma nasarori masu yawa a fannin cin gajiyar juna.

Sin da Afirka, sun ci gaba da raya dangantakar su, da wanzar da adalci a harkokin da suka shafi kasa da kasa, sun kuma rungumi ci gaban su cikin hadin gwiwa, suna yaki da kamfar abinci, yayin da Sin ke taimakawa kasashen yankin kahon Afirka dake fama da fari da abinci gwargwadon karfin ta, kana sassan 2 suna aiki tare wajen yaki da annobar COVID-19, da sauran matsalolin lafiya da sai sauran su. Alal misali, kasar Sin ta taimakawa AU wajen gina wata cibiyar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Ko da a baya bayan nan ma, wata tawagar jamian lafiya ta Sin, ta tashi daga birnin Shijiazhuang, fadar mulkin lardin Hebei na arewacin kasar Sin, zuwa janhuriyar dimokaradiyyar Congo. Tawagar da aka tsara za ta yi aikin tallafawa harkokin kiwon lafiya a kasar na tsawon shekara daya.

A bana ake ciki shekaru 50, tun bayan da lardin Hebei na kasar Sin, ya fara tura jamian lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen waje. Kuma tun fara gudanar da wannan muhimmin aiki ya zuwa yanzu, lardin na Hebei ya tura rukunonin jamian lafiya 21 zuwa janhuriyar dimokaradiyyar Congo.

Wannan dai bangare daya ne kawai, cikin muhimman fannoni da Sin ke samarwa kasashen Afirka taimako, karkashin alkawuran da Sin din ke yiwa ’yan uwan ta kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afirka. Don haka a iya cewa, kasar Sin na cika alkawura da take dauka ga kasashen Afirka yadda ya kamata. (Saminu Hassan)

Alkawari
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Zan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Gyara Tattalin Arzikin Nijeriya – Peter Obi

Ka Da A Mika Ragamar Mulkin Nijeriya A Hannun Mara Lafiya - Peter Obi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.