ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyawun Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
4 years ago
Alkawari

A watan Nuwambar shekarar 2021 ne aka gudanar da taro karo na 8, na ministocin kasashe mambobin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ko FOCAC, ta kafar bidiyo daga Dakar na kasar Senegal. 

Yayin taron, an amince da wasu manufofi, ciki har da yarjejeniyar Dakar. A kuma lokacin ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da kaddamar da wasu shirye shirye guda 9, na raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

  • Kwamitin Kula Da Ladabtarwa Da Sanya Ido Na Kwamitin Kolin JKS Ya Tsara Dabarun Daukar Kwararan Matakai Wajen Tafiyar Da Harkokin Jam’iyya Bisa Tsauraran Matakan Da’a

Masharhanta na kallon wannan shirye shirye a matsayin ginshikai da zai kara karfafa kawancen gargajiya tsakanin Sin da Afirka, za su kuma ingiza burin da ake da shi, na gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya a sabon zamani da muke ciki.

ADVERTISEMENT

Yanzu haka, an shafe shekara daya ko fiye tun bayan gudanar da wancan taro na ministoci. Kuma duk da cewa an samu manyan sauye-sauye a harkokin kasa da kasa, da tarin kalubale, da yanayi na rashin tabbas a wasu sassa, a daya bangaren Sin da kasashen Afirka, sun ci gaba da aiwatar da matakan goyawa juna baya, da zurfafa kyakkaywar alakar su yadda ya kamata. Kaza lika sassan biyu sun cimma nasarori masu yawa a fannin cin gajiyar juna.

Sin da Afirka, sun ci gaba da raya dangantakar su, da wanzar da adalci a harkokin da suka shafi kasa da kasa, sun kuma rungumi ci gaban su cikin hadin gwiwa, suna yaki da kamfar abinci, yayin da Sin ke taimakawa kasashen yankin kahon Afirka dake fama da fari da abinci gwargwadon karfin ta, kana sassan 2 suna aiki tare wajen yaki da annobar COVID-19, da sauran matsalolin lafiya da sai sauran su. Alal misali, kasar Sin ta taimakawa AU wajen gina wata cibiyar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Ko da a baya bayan nan ma, wata tawagar jamian lafiya ta Sin, ta tashi daga birnin Shijiazhuang, fadar mulkin lardin Hebei na arewacin kasar Sin, zuwa janhuriyar dimokaradiyyar Congo. Tawagar da aka tsara za ta yi aikin tallafawa harkokin kiwon lafiya a kasar na tsawon shekara daya.

A bana ake ciki shekaru 50, tun bayan da lardin Hebei na kasar Sin, ya fara tura jamian lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen waje. Kuma tun fara gudanar da wannan muhimmin aiki ya zuwa yanzu, lardin na Hebei ya tura rukunonin jamian lafiya 21 zuwa janhuriyar dimokaradiyyar Congo.

Wannan dai bangare daya ne kawai, cikin muhimman fannoni da Sin ke samarwa kasashen Afirka taimako, karkashin alkawuran da Sin din ke yiwa ’yan uwan ta kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afirka. Don haka a iya cewa, kasar Sin na cika alkawura da take dauka ga kasashen Afirka yadda ya kamata. (Saminu Hassan)

Alkawari
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Zan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Gyara Tattalin Arzikin Nijeriya – Peter Obi

Ka Da A Mika Ragamar Mulkin Nijeriya A Hannun Mara Lafiya - Peter Obi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.