Jam’iyyar APC ta kammala zaɓen fidda gwani na ‘yan takarar Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, inda Kakakin Majalisar, Haruna Dangyatin, da sauran manyan ‘yan majalisar suka samu tikitin sake tsayawa takara gabanin zaɓen shekarar 2027.
Sai dai kuma, ‘yan majalisa masu ci guda takwas sun gaza samun tikitin komawa majalisar a ƙarƙashin jam’iyyar APC.
An gudanar da zaɓen cikin lumana a dukkan mazaɓu 30 na jihar a ranar Asabar, inda aka tabbatar da ‘yan takarar da jam’iyyar ta riga ta amince da su ta hanyar maslaha.
Waɗanda suka rasa tikitin jam’iyyar sun haɗa da Abubakar Sadiq Muhammad Jallo (Hadejia), Mas’ud Abdulrahman Naruwa (Babura), Idris Garba na Jahun, Ibrahim Ya’u na Gagarawa, Aliyu Ahmad Aliyu na Kiri-Kasamma, Muhammad Adamu na Kafin Hausa, Yusuf Ahmed na Bulangu da Aminu Sule na Ringim.
An tabbatar da tikitin Kakakin Majalisar, Haruna Dangyatin, ne a hedikwatar ƙaramar hukumar Miga a gaban jami’an tsaro, wakilan Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), wakilan APC daga hedikwatar jam’iyyar ta ƙasa da kuma ‘yan jarida.















Discussion about this post