Mai fafutukar kare hakkin bil’adama kuma ɗan siyasa, Omoyele Sowore, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su fito zanga-zanga a faɗin ƙasar nan ranar Litinin domin nuna rashin gamsuwarsu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.
Sowore ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Lahadi, kwanaki kaɗan bayan rahotannin da suka ce an kwantar da shi a asibiti sakamakon artabu da jami’an tsaro yayin zanga-zangar Ranar Dimokuraɗiyya a Abuja.
A cikin saƙon, Sowore ya buƙaci jama’a su taru a birane, da garuruwa da sauran wuraren taruwar jama’a domin neman a sauke Tinubu daga mulki. Ya ce dole ne muryar ‘yan Nijeriya ta fito fili domin nuna adawa da yadda ake tafiyar da mulki.
Kiran nasa na zuwa ne bayan Amnesty International ta soki abin da ta kira murƙushe masu zanga-zangar lumana a Abuja, tana mai nuna damuwa kan yadda jami’an tsaro suka daƙile masu zanga-zangar.














Discussion about this post