Rundunar ƴansanda ta ƙasa reshan jihar Zamfara ta gano tare da tarwatsa wani bam na IED da ake zargin ‘yan bindiga ne suka dasa a hanyar Kunchin Kalgo da ke ƙaramar hukumar Tsafe, lamarin da ya hana aukuwar wani mummunan hari da zai iya jawo asarar rayuka masu yawa.
Kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya ce jami’an VCRU tare da sashin EOD sun gudanar da aikin ne da misalin ƙarfe 4:15 na yammacin ranar 13 ga Yuni, 2026, bayan samun sahihan bayanai daga mazauna yankin kan wasu motsi masu tayar da hankali a’a yankin.
A cewarsa, an dasa bam ɗin ne da nufin kai hari kan matafiya da masu amfani da hanyar, amma gaggawar da jami’an tsaro suka yi ta hana afkuwar mummunan lamarin. Ya ce haɗin kan al’umma da jami’an tsaro na ci gaba da taimakawa wajen dakile hare-hare kafin su faru.
Rundunar ta ce bincike na ci gaba domin gano waɗanda suka dasa bam ɗin tare da cafke su, yayin da aka ƙara sintiri da rakiyar jami’an tsaro a manyan hanyoyi da sauran wuraren da ake ganin suna da haɗari a faɗin jihar.















Discussion about this post