Shugaban kasar Mongoliya Ukhnaa Khurelsukh ya zanta da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a jiya Asabar. Yayin zantawar tasu, shugaba Khurelsukh ya ce, alakar Mongoliya da Sin misali ne na kyakkyawar dangantaka tsakanin kasashe biyu dake shiyya daya.
Ya ce kasashen biyu sun jima suna martaba ‘yancin kai, da ikon mulkin yankunansu. A daya bangaren kuma, suna zurfafa hadin gwiwa na cimma moriyar bai daya a sassa daban daban. Kuma a shekarar bana, ana sa ran darajar cinikayya tsakanin kasashen biyu za ta kai dalar Amurka biliyan 20.
Bugu da kari, shugaba Khurelsukh ya ce, Mongoliya na martaba manufar nan ta kasar Sin daya tak a duniya, tana daukar yankin Taiwan a matsayin bangaren Sin da ba za a iya balle shi ba, kana tana adawa da duk wasu ayyuka masu nasaba da “Neman ‘yancin kan Taiwan”. Har ila yau, tana kallon batutuwa masu nasaba da yankin Hong Kong, da Xizang da Xinjiang, a matsayin harkokin cikin gidan kasar Sin.
Kuma Mongoliya ba za ta aiwatar da duk wani mataki da zai illata moriyar kasar Sin ba, ko da kuwa yaya alakar kasar take da wasu kasashen na daban.A nasa bangare kuwa, Wang Yi cewa ya yi har kullum kasar Sin na daukar alakarta da Mongoliya da matukar muhimmanci karkashin diflomasiyyar makwaftaka, kuma Sin na da nufi, da ikon zama makwafciya da Mongoliya za ta iya dogaro da ita.
Za kuma ta ci gaba da zama kawa ta gari, kana abokiyar hulda a fanin hanzarta samar da ci gaba.A wani ci gaban kuma, a dai jiyan, Wang Yi ya zanta da ministar harkokin wajen kasar ta Mongoliya Batmunkh Battsetseg. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post