Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya soki shirin Gwamnatin Tarayya na karɓo sabon bashi domin biyan basussukan ɓangaren wutar lantarki, yana mai cewa hakan na nuna rashin tsari da rashin cikakken bayani kan yadda ake tafiyar da kuɗaɗen gwamnati.
Atiku ya ce ‘yan Nijeriya na da haƙƙin sanin yadda aka kashe kuɗaɗen da aka karɓo a baya domin warware matsalolin ɓangaren wutar lantarki, yana mai tambayar dalilin da ya sa har yanzu matsalar bashin ɓangaren ke ci gaba da taruwa duk da tarin bashikan da aka ciyo a baya.
Ya bayyana shirin bond na Naira biliyan 590 da aka sanar a 2025, da wani na Naira biliyan 501, da kuma shirin Naira tiriliyan 3.3 da aka amince da shi a 2026, yana mai cewa duk waɗannan ba su haifar da gagarumin sauyi a samar da lantarki ba.
Atiku ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta bayyana adadin kuɗaɗen da aka tara, da yadda aka kashe su, da waɗanda aka biya da kuma bashin da har yanzu ake bi kafin a sake ɗaukar wani sabon bashi a ɓangaren lantarki.















Discussion about this post