Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya ce jigon alakar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Amurka shi ne cin moriyar juna da samun nasara tare.
Ya kamata bangarorin biyu su aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma da kuma kawo karin daidaito da kwanciyar hankali ga hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayyarsu da ma cinikayyar duniya.
Guo ya bayyana hakan ne yayin da yake ba da amsar wata tambaya game da dangantakar tattalin arziki da cinikayyar Sin da Amurka a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka yi yau Talata.
Dangane da takunkumin da baitil-malin Amurka ta sanya kwanan nan kan mutane da kamfanoni da ake zargin cewa suna da alaka da Iran, ciki har da wasu kamfanonin yankin Hong Kong, Guo ya bayyana cewa bangaren Sin ya nuna adawa da takunkumi da ake kakabawa daga bangare daya ba tare da wata hujja a cikin dokokin kasa da kasa, ko izini daga kwamitin sulhu na MDD ba. Ya kuma bayyana cewa babban aikin da ya fi bukatar gaggawa game da halin da ake ciki a Iran shi ne yin iyakacin kokarin hana sake barkewar yaki, maimakon yi wa Sin batanci.
Bugu da kari, yayin da yake ba da amsar tambayar da ta shafi ziyarar aiki da shugaba Donald Trump zai yi a Sin, Guo ya ce, yayin ziyararsa a Sin, shugabannin kasashen biyu za su yi musayar ra’ayoyi masu zurfi kan manyan batutuwa da suka shafi dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma batutuwan da suka shafi zaman lafiya da ci gaban duniya. Matsayin Sin kan adawa da sayar wa yankin Taiwan makamai da Amurka ke yi abu ne da ya dace kuma a bayyane yake.(Safiyah Ma)















Discussion about this post