Wani ɗan kunar baƙin wake da ke cikin keken adaidaita (keke-napep) ɗauke da abubuwan fashewa ya kashe aƙalla mutane tara tare da jikkata wasu 34 a arewa maso yammacin Pakistan a ranar Talata, kamar yadda ‘yansanda suka bayyana.
“Bisa ga rahotannin farko, wanda ake zargin ɗan kunar baƙin waken ne, ya kusanci jami’an ‘yansanda dake bakin aiki a wurin binciken ababen hawa, sannan ya tayar da bam ɗin da ke jikinsa,” in ji wani babban jami’in ‘yansanda, Muhammad Sajjad Khan, yayin da yake magana da kafar yada labarai ta AFP.
Wannan harin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan wani makamancin irin wannan harin na kunar baƙin wake inda wata mota ɗauke da bam ta fashe a wani wurin bincike a Bannu kafin ‘yan bindiga su buɗe wuta kan ‘yansanda, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 15.
Ma’aikatar harkokin wajen Pakistan ta gayyaci babban jami’in diflomasiyyar Afghanistan da ke ƙasar a ranar Litinin bayan ta kammala binciken cewa, harin da aka kai ranar Asabar “’yan ta’addan da ke zaune a Afghanistan ne suka shirya shi.”
Sai dai gwamnatin Taliban ta Afghanistan ta sha musanta zargin Pakistan cewa ana amfani da ƙasar Afghanistan a matsayin mafakar ‘yan ta’adda.















Discussion about this post