Yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.
Yayin da wani dan jarida ya yi masa tambaya game da abun da Japan ke yayatawa cewa wai Sin ta yi amfani da na’urar radar kan jiragen saman yaki na Japan, Guo ya ba da amsa cewa: “Ina ba ’yan jarida shawarar su tambayi bangaren Japan dalilin da ya sa jiragen saman yaki na sojojinta suka shiga yankin don haifar da wannan lamari mai hadari wanda bai kamata ya faru ba. Shin yunkuri ne na kawo cikas ga ayyukan horo na yau da kullun na Sin da gangan, da kuma haifar da tashin hankali?”
Game da kalamai marasa dacewa da firaministar Japan Takaichi Sanae ta yi kan yankin Taiwan na Sin, Guo ya ce, yin sassauci ga kalamai da ayyukan cin zarafi da Japan ke yi, zai sake haifar da farfadowar ra’ayin nuna karfin soja.
Dangane da rikicin da ya faru kwanan nan tsakanin sojojin Afghanistan da Pakistan, Guo Jiakun ya ce Sin na kira ga kasashen biyu da su ci gaba da warware sabanin da ke tsakaninsu ta hanyar tattaunawa, tare da hada hannu don kare zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Dangane da sanarwar da Amurka ta yi cewa za ta bai wa kamfanin NVIDIA damar sayar da kananan na’urorin lantarki na fasahar AI samfurin NVIDIA HGX H200 ga Sin, Guo Jiakun ya ce Sin ta dade tana goyon bayan Sin da Amurka su samu moriyar juna da cimma nasara tare ta hanyar hadin gwiwa.(Safiyah Ma)














