Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce sojojin Nijeriya ba za su iya yin galaba a kan ’yan bindiga ta hanyar yaƙi kaɗai ba.
Gumi, ya ce gwamnati ya kamata ta tattauna da ’yan bindiga idan tana son rage matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya.
- Ma’aikatar Wajen Sin: Shin Japan Tana Yunkurin Ci Zarafin Sin Tare Da Haifar Da Tashin Hankali
- Ƙalubalen Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Shi Da Alaƙa Da Addini — Gwamnatin Tarayya
Da yake magana da BBC, ya bayyana cewa duk duniya sojoji kan sha wahala wajen yaƙar ‘yan ta’adda amma ba su cika yin nasara ba.
Ya ce: “Ko sojojin kansu sun amince cewa kashi 25 ne kawai za a iya yi da ƙarfin bindiga. Sauran aikin ya dogara ne ga gwamnati, siyasa da kuma al’ummomi. Sojoji ba za su iya yin komai su kaɗai ba.
“A ina ka taɓa ganin sojoji sun kawo ƙarshen ‘yan ta’adda? Babu inda hakan ta faru.”
Maganganun Gumi na zuwa ne bayan da Shugaba Bola Tinubu ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da an kuɓutar da duk mutanen da ’yan ta’adda suka sace.
Tinubu ya kuma bukaci jami’an tsaro su yi aiki tare da gwamnonin jihohi domin ganin an saki waɗanda aka yi garkuwa da su.














