ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafarkin Kasashen Afrika Zai Tabbata Albarkacin Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Afrika

A lokacin da taro na 4 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wadda ke zaman majalisar dokokin kasar ke gudana a birnin Beijing, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya kira taron manema labarai a jiya Lahadi, inda ya yi karin haske kan manufofin diplomasiyyar kasar Sin.

Mun riga mun san cewa, burin kasar Sin har kullum shi ne, zaman tare bisa adalci da daidaito da hakuri da girmama juna da kuma samun ci gaba na bai daya a duniya.

Da aka yi masa tambaya game da irin sabbin ci gaban da za a gani a dangantakar Sin da Afrika a bana, Wang Yi ya bayyana wasu batutuwa 3:

ADVERTISEMENT

Na farko, al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Afrika. Wannan na nufin bangarorin biyu sun zarce abokan hulda kawai, abokai ne da za su rika tafiya tare kafada da kafada a kan tafarki daya na samun ci gaba. Haka kuma yana nufin Sin za ta kasance babbar yaya wajen jagorantar kasashen Afrika su lalubo hanyar da ta dace da su ta samu ci gaba da kuma dogaro da kansu. Wannan ya nuna cewa, Sin tana son kasashen Afrika su kasance masu tsayawa da kafarsu, masu karfin fada a ji kan lamuran da suka shafe su, haka kuma masu bijerewa baba-kere da cin zali. Wanda zai taimaka matuka wajen ganin sun amfanawa kansu da kansu ba tare da neman taimako mai tattare da sharuda da katsalandan ba.

Batu na biyu shi ne, soke harajin kwastam. A duniyar dake fama da rikicin cinikayya da karuwar harajin fito, ba tare da la’akari da matsayin kasashen Afrika na masu tasowa ba, Sin ta kara nuna matsayinta na babbar yaya, ta soke haraji kan kayayyakin kasashen Afrika 53 dake da huldar diplomasiyya da ita. Abun nufi, kasar Sin ta bude kofarta da katafariyar kasuwarta ga kasashen Afrika su shigo su ci gajiya. A ko da yaushe burin kasashen shi ne, su tashi daga masu dogaro da kayayyaki daga kasashen waje, su zama masu sarrafawa da fitar da kayayyaki. Kuma a bana, mafarkinsu zai tabbata albarkacin kasar Sin. Wannan abu ne da zai karfafa takardun kudinsu da bunkasa masana’antu da ayyukan gona, wadanda za su samar da aikin yi. Idan hakan ta samu kuma, arziki zai wadata a cikin al’umma, kuma za a samu raguwar aikata laifuka da tabbatuwar zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Batu na 3, aiwatar da shirye-shirye 600 na musayar al’adu tsakanin Sin da Afrika. Fahimtar juna ita ce kashin bayan kowane mu’amala. Yayin da ake samun habakar hulda ta cinikayya da tattalin arziki, ya zama wajibi a fahimci juna tsakanin mabambantan al’ummomi domin kaucewa rigingimu. Musaya tsakanin Sin da Afrika za ta bayar da muhimmiyar gudunmawa ga burin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Za ta kara kyautata mu’amala tsakanin al’ummominsu, haka kuma, za ta toshe duk wata kafa da masu yada jita-jita ke amfani da ita ta haddasa fitina.

Idan muka nazarci wadannan batutuwa da ya zayyano, a dunkule abubuwa ne da za su inganta ci gaban kasashen Afrika da bude musu kofar samun karin wadata. Hakika ci gaban Sin, ci gaba ne ga nahiyar Afrika. Kasar Sin ta zama jagora mai haskawa kasashen Afrika hanyar samun ci gaban da suke buri. (FMM)

 

 

Afrika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Afrika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Kamfanonin Kasa Da Kasa Sun Nuna Gamsuwa Da Dimbin Damarmakin Da Kasuwar Kasar Sin Ta Samar

Kamfanonin Kasa Da Kasa Sun Nuna Gamsuwa Da Dimbin Damarmakin Da Kasuwar Kasar Sin Ta Samar

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.