ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafarkin Kasashen Afrika Zai Tabbata Albarkacin Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Afrika

A lokacin da taro na 4 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wadda ke zaman majalisar dokokin kasar ke gudana a birnin Beijing, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya kira taron manema labarai a jiya Lahadi, inda ya yi karin haske kan manufofin diplomasiyyar kasar Sin.

Mun riga mun san cewa, burin kasar Sin har kullum shi ne, zaman tare bisa adalci da daidaito da hakuri da girmama juna da kuma samun ci gaba na bai daya a duniya.

Da aka yi masa tambaya game da irin sabbin ci gaban da za a gani a dangantakar Sin da Afrika a bana, Wang Yi ya bayyana wasu batutuwa 3:

ADVERTISEMENT

Na farko, al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Afrika. Wannan na nufin bangarorin biyu sun zarce abokan hulda kawai, abokai ne da za su rika tafiya tare kafada da kafada a kan tafarki daya na samun ci gaba. Haka kuma yana nufin Sin za ta kasance babbar yaya wajen jagorantar kasashen Afrika su lalubo hanyar da ta dace da su ta samu ci gaba da kuma dogaro da kansu. Wannan ya nuna cewa, Sin tana son kasashen Afrika su kasance masu tsayawa da kafarsu, masu karfin fada a ji kan lamuran da suka shafe su, haka kuma masu bijerewa baba-kere da cin zali. Wanda zai taimaka matuka wajen ganin sun amfanawa kansu da kansu ba tare da neman taimako mai tattare da sharuda da katsalandan ba.

Batu na biyu shi ne, soke harajin kwastam. A duniyar dake fama da rikicin cinikayya da karuwar harajin fito, ba tare da la’akari da matsayin kasashen Afrika na masu tasowa ba, Sin ta kara nuna matsayinta na babbar yaya, ta soke haraji kan kayayyakin kasashen Afrika 53 dake da huldar diplomasiyya da ita. Abun nufi, kasar Sin ta bude kofarta da katafariyar kasuwarta ga kasashen Afrika su shigo su ci gajiya. A ko da yaushe burin kasashen shi ne, su tashi daga masu dogaro da kayayyaki daga kasashen waje, su zama masu sarrafawa da fitar da kayayyaki. Kuma a bana, mafarkinsu zai tabbata albarkacin kasar Sin. Wannan abu ne da zai karfafa takardun kudinsu da bunkasa masana’antu da ayyukan gona, wadanda za su samar da aikin yi. Idan hakan ta samu kuma, arziki zai wadata a cikin al’umma, kuma za a samu raguwar aikata laifuka da tabbatuwar zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Batu na 3, aiwatar da shirye-shirye 600 na musayar al’adu tsakanin Sin da Afrika. Fahimtar juna ita ce kashin bayan kowane mu’amala. Yayin da ake samun habakar hulda ta cinikayya da tattalin arziki, ya zama wajibi a fahimci juna tsakanin mabambantan al’ummomi domin kaucewa rigingimu. Musaya tsakanin Sin da Afrika za ta bayar da muhimmiyar gudunmawa ga burin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Za ta kara kyautata mu’amala tsakanin al’ummominsu, haka kuma, za ta toshe duk wata kafa da masu yada jita-jita ke amfani da ita ta haddasa fitina.

Idan muka nazarci wadannan batutuwa da ya zayyano, a dunkule abubuwa ne da za su inganta ci gaban kasashen Afrika da bude musu kofar samun karin wadata. Hakika ci gaban Sin, ci gaba ne ga nahiyar Afrika. Kasar Sin ta zama jagora mai haskawa kasashen Afrika hanyar samun ci gaban da suke buri. (FMM)

 

 

Afrika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Afrika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kamfanonin Kasa Da Kasa Sun Nuna Gamsuwa Da Dimbin Damarmakin Da Kasuwar Kasar Sin Ta Samar

Kamfanonin Kasa Da Kasa Sun Nuna Gamsuwa Da Dimbin Damarmakin Da Kasuwar Kasar Sin Ta Samar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.