Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Sokoto ta sanar da cewa, mahajjata 2,235 ne suka yi rajista don zuwa aikin Hajjin 2026.
Hukumar ta kuma tabbatar da cewa shirye-shirye sun yi nisa don tabbatar da gudanar da aikin hajjin cikin nutsuwa, mai tsari kuma gamsasshe ga dukkan mahajjatan.
- Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
- Rikicin PDP Ne Ya Sanya Ni Komawa Jam’iyyar Accord – Adeleke
Da yake magana da manema labarai a sakatariyar hukumar da ke Sokoto, Shugaban Hukumar, Alhaji Ali Musa, ya tabbatar da cewa an kammala manyan shirye-shirye domin tunkarar aikin hajjin na bana.
A cewar Musa, shirye-shiryen sun hada da jigilar kayayyakin tafiya, masaukai da kammala yarjejeniyar ciyarwa da hukumomin da suka dace a Kasar ta Saudiyya.
A cewarsa, adadin mahajjatan da suka yi rajistar ya hada har da jami’an gwamnati.














