ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Al’ummun Afirka Dangane Da Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanya Tsakanin Al’ummun Sin Da Na Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
5 months ago
Afirka

Bayan kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka a shekarar nan ta 2026, masharhanta  da dama musamman daga kasashen Afirka, na ganin an dauki wata hanya ta kara raya cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka, wanda hakan ke nuni ga fadada alakar sassan biyu daga samar da ababen more rayuwa, da bunkasa hada-hadar cinikayya zuwa zurfafa sada zumunta, da raya zamantakewar al’ummun sassan biyu.

Ko shakka babu, bunkasa musaya tsakanin al’ummun Sin da na kasashen Afirka zai yaukaka amincewa da fahimtar juna, da raba kwarewa a fannin sanin makamar aiki musamman ga al’ummun kasashen Afirka masu tasowa. Karkashin wannan manufa, dalibai, da matasa, da kwararru da masu sana’o’i, da masu bincike, da ma’aikatan kafofin watsa labarai za su samu zarafin cudanya kai tsaye, tare da gane yadda bangarorin biyu ke gudanar da manufofin raya ci gaban al’umma. Kuma sannu a hankali, za su kai ga bude sabbin babuka na hadin gwiwa mai dorewa.

A gani na wani abu da ya bambanta sabuwar manufar nan ta raya musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka, da manufofi makamantanta na baya, shi ne dora karin muhimmanci kan ci gaban al’ummu, da cudanyar jama’a a matakin farko. Wannan kari ne kan manufofin baya, na samar da ababen more rayuwa, irinsu hanyoyin mota, da layukan dogo, da hakar ma’adanai da hada-hadar kudade da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka a shekarar nan ta 2026, ya zamo jigon mayar da karin matasan nahiyar Afirka masu dogaro da kai, kana za a kai ga raya al’adu, da ilimi da kafafen watsa labarai. Har ila yau, karkashin hakan an tsara aiwatar da ayyuka kusan 600, matakin dake nuni ga shirin wanzar da aniyar raya zamantakewar al’ummun Afirka cikin dogon lokaci, wanda hakan na da matukar muhimmanci ga cimma nasarar bunkasa cinikayya, da zuba jari, da hadin gwiwar samun ci gaban bai daya na shekaru masu yawa a nan gaba.

A kasashen Afirka, wannan manufa za ta samar da muhimman damammaki na raya sanin makamar aiki, musamman a gabar da kasashen nahiyar ke ta kokarin fadada hanyoyin raya tattalin arzikinsu, da neman hanyoyin magance kalubalen kamfar guraben ayyukan yi tsakanin matasa.

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Ko shakka babu wannan manufa ta musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka za ta taimaka kwarai wajen gina kwarewar ayyuka, da horar da matasa, da musayar ilimi a muhimman sassa. A daya bangaren kasashen Afirka, za su iya yin koyi daga kwarewar Sin a fagen bunkasa masana’antu, da fasahohin dijital, da yawon bude ido, da bunkasa kananan sana’o’i da dai sauransu.

Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

MASU ALAKA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Next Post
Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Har Lahira A Neja

Ɗalibin Jami'a Ya Hallaka Kansa Har Lahira A Neja

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.