ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Al’ummun Afirka Dangane Da Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanya Tsakanin Al’ummun Sin Da Na Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 months ago
Afirka

Bayan kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka a shekarar nan ta 2026, masharhanta  da dama musamman daga kasashen Afirka, na ganin an dauki wata hanya ta kara raya cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka, wanda hakan ke nuni ga fadada alakar sassan biyu daga samar da ababen more rayuwa, da bunkasa hada-hadar cinikayya zuwa zurfafa sada zumunta, da raya zamantakewar al’ummun sassan biyu.

Ko shakka babu, bunkasa musaya tsakanin al’ummun Sin da na kasashen Afirka zai yaukaka amincewa da fahimtar juna, da raba kwarewa a fannin sanin makamar aiki musamman ga al’ummun kasashen Afirka masu tasowa. Karkashin wannan manufa, dalibai, da matasa, da kwararru da masu sana’o’i, da masu bincike, da ma’aikatan kafofin watsa labarai za su samu zarafin cudanya kai tsaye, tare da gane yadda bangarorin biyu ke gudanar da manufofin raya ci gaban al’umma. Kuma sannu a hankali, za su kai ga bude sabbin babuka na hadin gwiwa mai dorewa.

A gani na wani abu da ya bambanta sabuwar manufar nan ta raya musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka, da manufofi makamantanta na baya, shi ne dora karin muhimmanci kan ci gaban al’ummu, da cudanyar jama’a a matakin farko. Wannan kari ne kan manufofin baya, na samar da ababen more rayuwa, irinsu hanyoyin mota, da layukan dogo, da hakar ma’adanai da hada-hadar kudade da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka a shekarar nan ta 2026, ya zamo jigon mayar da karin matasan nahiyar Afirka masu dogaro da kai, kana za a kai ga raya al’adu, da ilimi da kafafen watsa labarai. Har ila yau, karkashin hakan an tsara aiwatar da ayyuka kusan 600, matakin dake nuni ga shirin wanzar da aniyar raya zamantakewar al’ummun Afirka cikin dogon lokaci, wanda hakan na da matukar muhimmanci ga cimma nasarar bunkasa cinikayya, da zuba jari, da hadin gwiwar samun ci gaban bai daya na shekaru masu yawa a nan gaba.

A kasashen Afirka, wannan manufa za ta samar da muhimman damammaki na raya sanin makamar aiki, musamman a gabar da kasashen nahiyar ke ta kokarin fadada hanyoyin raya tattalin arzikinsu, da neman hanyoyin magance kalubalen kamfar guraben ayyukan yi tsakanin matasa.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Ko shakka babu wannan manufa ta musayar al’adu da cudanya tsakanin al’ummun Sin da na nahiyar Afirka za ta taimaka kwarai wajen gina kwarewar ayyuka, da horar da matasa, da musayar ilimi a muhimman sassa. A daya bangaren kasashen Afirka, za su iya yin koyi daga kwarewar Sin a fagen bunkasa masana’antu, da fasahohin dijital, da yawon bude ido, da bunkasa kananan sana’o’i da dai sauransu.

Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Har Lahira A Neja

Ɗalibin Jami'a Ya Hallaka Kansa Har Lahira A Neja

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.