ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Fara Yunƙurin Gyaran Dokokin Soja

by Sulaiman
3 weeks ago

Majalisar Wakilai ta Tarayya ta fara nazarin wasu muhimman ƙudurorin dokoki da suka shafi harkokin tsaro, da nufin ƙarfafa tsarin rundunonin sojin Nijeriya, inganta walwalar jami’an soja da tsofaffin sojoji, da kuma ƙara wa rundunar ƙarfi wajen tunkarar sabbin barazanar tsaro.

Da yake jawabi a taron sauraron ra’ayoyin jama’a na kwanaki biyu da Kwamitin Tsaro na Majalisar ya shirya a Abuja, Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce an tsara ƙudurorin ne domin magance sauye-sauyen ƙalubalen tsaro da kuma gina rundunar soja mai ƙarfi da tasiri.

Ya bayyana cewa ƙudurorin sun yi daidai da manufofin Majalisar Wakilai ta 10, kuma suna nuna ƙudirin ƴan majalisa na sake fasalin bangaren tsaron ƙasa.Abbas ya ce sabbin barazanar tsaro kamar fashin teku a yankin Tekun Guinea, yaƙin da damfara a Intanet, da haɗin gwiwar masu aikata manyan laifuka da ƴan ta’adda, sun ƙara nuna buƙatar yin gyare-gyare masu zurfi a fannin tsaro.Daga cikin manyan ƙudurorin da ake dubawa akwai: Dokar Shirin Gonaki da Kiwon Dabbobi na Rundunar Soji, wadda ke da nufin haɗa tsaron abinci da ayyukan soja, musamman a yankunan da ake fama da rikice-rikice.

ADVERTISEMENT

Dokar Wakilcin Mata a Rundunar Soji, domin ƙarfafa ba mata damar shiga aikin soja da samun wakilci mai kyau.Dokar Rundunar Sojin Nijeriya, wadda za ta soke tare da maye gurbin tsohuwar Dokar Rundunar Soji domin dacewa da yanayin zamani.

Dokar Ƙungiyar Tsofaffin Sojojin Nijeriya, da ke neman inganta walwala da jin daɗin tsofaffin jami’an soja.Kakakin Majalisar ya buƙaci masu ruwa da tsaki, ciki har da jami’an soja masu aiki da waɗanda suka yi ritaya, ƙungiyoyin farar hula, masu fafutukar kare haƙƙin mata, lauyoyi da sauran jama’a da su bayar da gudunmawarsu a wannan tsari na doka.

LABARAI MASU NASABA

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

Tun da farko, shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Wakilai, Babajimi Benson, ya bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ga ƴan ƙasa da masu ruwa da tsaki su bayar da gudunmawa wajen tsara dokokin da za su ƙarfafa tsarin tsaro da kariyar Nijeriya.

Ya ce ƙudurorin sun shafi muhimman fannoni kamar ilimin soja da horar da jami’ai, inganta haɗin gwiwar ayyukan tsaro, kiwon lafiya, bincike da dabarun soja, walwalar tsofaffin sojoji, gyaran tsarin gudanarwa, tsaron abinci da kuma ƙarfafa shigar mata a rundunar soji.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba
Labarai

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai
Labarai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Next Post
Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

LABARAI MASU NASABA

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.