ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Fara Yunƙurin Gyaran Dokokin Soja

by Sulaiman
2 hours ago

Majalisar Wakilai ta Tarayya ta fara nazarin wasu muhimman ƙudurorin dokoki da suka shafi harkokin tsaro, da nufin ƙarfafa tsarin rundunonin sojin Nijeriya, inganta walwalar jami’an soja da tsofaffin sojoji, da kuma ƙara wa rundunar ƙarfi wajen tunkarar sabbin barazanar tsaro.

Da yake jawabi a taron sauraron ra’ayoyin jama’a na kwanaki biyu da Kwamitin Tsaro na Majalisar ya shirya a Abuja, Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce an tsara ƙudurorin ne domin magance sauye-sauyen ƙalubalen tsaro da kuma gina rundunar soja mai ƙarfi da tasiri.

Ya bayyana cewa ƙudurorin sun yi daidai da manufofin Majalisar Wakilai ta 10, kuma suna nuna ƙudirin ƴan majalisa na sake fasalin bangaren tsaron ƙasa.Abbas ya ce sabbin barazanar tsaro kamar fashin teku a yankin Tekun Guinea, yaƙin da damfara a Intanet, da haɗin gwiwar masu aikata manyan laifuka da ƴan ta’adda, sun ƙara nuna buƙatar yin gyare-gyare masu zurfi a fannin tsaro.Daga cikin manyan ƙudurorin da ake dubawa akwai: Dokar Shirin Gonaki da Kiwon Dabbobi na Rundunar Soji, wadda ke da nufin haɗa tsaron abinci da ayyukan soja, musamman a yankunan da ake fama da rikice-rikice.

ADVERTISEMENT

Dokar Wakilcin Mata a Rundunar Soji, domin ƙarfafa ba mata damar shiga aikin soja da samun wakilci mai kyau.Dokar Rundunar Sojin Nijeriya, wadda za ta soke tare da maye gurbin tsohuwar Dokar Rundunar Soji domin dacewa da yanayin zamani.

Dokar Ƙungiyar Tsofaffin Sojojin Nijeriya, da ke neman inganta walwala da jin daɗin tsofaffin jami’an soja.Kakakin Majalisar ya buƙaci masu ruwa da tsaki, ciki har da jami’an soja masu aiki da waɗanda suka yi ritaya, ƙungiyoyin farar hula, masu fafutukar kare haƙƙin mata, lauyoyi da sauran jama’a da su bayar da gudunmawarsu a wannan tsari na doka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

Tun da farko, shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Wakilai, Babajimi Benson, ya bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ga ƴan ƙasa da masu ruwa da tsaki su bayar da gudunmawa wajen tsara dokokin da za su ƙarfafa tsarin tsaro da kariyar Nijeriya.

Ya ce ƙudurorin sun shafi muhimman fannoni kamar ilimin soja da horar da jami’ai, inganta haɗin gwiwar ayyukan tsaro, kiwon lafiya, bincike da dabarun soja, walwalar tsofaffin sojoji, gyaran tsarin gudanarwa, tsaron abinci da kuma ƙarfafa shigar mata a rundunar soji.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Sulaiman
    Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa
  • Sulaiman
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

MASU ALAKA

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya
Labarai

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Daga Ƙarshe, Tinubu Ya Naɗa Jakadu Uku Bayan Tsawon Shekara 2 Ana Jira
Labarai

Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa

June 19, 2026
Next Post
Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

June 19, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Majalisar Wakilai Ta Fara Yunƙurin Gyaran Dokokin Soja

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Daga Ƙarshe, Tinubu Ya Naɗa Jakadu Uku Bayan Tsawon Shekara 2 Ana Jira

Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa

June 19, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

June 19, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

June 18, 2026
Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

June 18, 2026
Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

June 18, 2026
Tinubu

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.