ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Iyalan Marigayiya Maimuna Sani (Nihal), ɗaliba mai shekaru 14 a aji biyu a karamar sakandare (JSS2) sashin makarantar kwana ta St. Louis da ke Kano, sun nemi a yi musu adalci bayan rasuwarta cikin yanayi mai cike da ruɗani da ake ta cece-kuce kan makarantar.

Iyalan yarinyar sun ce an ba su bayanai mabambanta kan musabbabin mutuwar Nihal. Yayin da makarantar ta ce ta rasu ne sakamakon tashin ciwon cutar asma, wasu bayanai sun nuna cewa an hukunta ta ne saboda jinkirin zuwa masallaci, inda ake zargin manyan ɗalibai mata sun yi mata bulala tare da tilasta mata yin durƙushe na tsawon lokaci kafin ta faɗi ta suma.

Mahaifiyarta, Nusaiba Rabiu Dan Sheriff, ta ce an kira iyalinsu zuwa asibiti inda aka tabbatar musu da mutuwar yarinyar. Ta bayyana cewa ma’aikatan asibitin sun tambaye su ko Nihal na fama da cutar asma, lamarin da ya ƙara jefa su cikin shakku. Ta kuma ce ta lura da wasu alamomi a jikin gawar ɗiyarta da suka sa ta fara tambayar ko an ɓoye mata wani abu game da abin da ya faru.

ADVERTISEMENT

Ta ce tana da yaƙinin akwai wasu bayanai da har yanzu ba a bayyana ba, saboda haka ta buƙaci gwamnati da hukumomin da abin ya shafa su gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar lamarin da kuma hukunta duk wanda aka samu da hannu a mutuwar yarinyar.

Da aka tuntuɓi shugabar makarantar, Reverend Sister Christiana Diyab, ta ce ba za ta yi magana kan lamarin ba a yanzu saboda yana hannun ‘yansanda. A nata ɓangaren, Rundunar ‘Yansandan Kano ta tabbatar da kafa kwamitin bincike na musamman bayan karɓar ƙorafi daga iyalan marigayiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

Daily Trust ta rawaito cewa, rundunar ta ce ta gayyaci malamai uku, manyan ɗalibai mata uku da wasu shaidu biyu domin bayar da bayani, yayin da ake ci gaba da gwaje-gwajen likitanci da na kimiyyar bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwar Nihal.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness
  • Abubakar Sulaiman
    NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN
Labarai

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Next Post
Manzon Allah

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.