Iyalan Marigayiya Maimuna Sani (Nihal), ɗaliba mai shekaru 14 a aji biyu a karamar sakandare (JSS2) sashin makarantar kwana ta St. Louis da ke Kano, sun nemi a yi musu adalci bayan rasuwarta cikin yanayi mai cike da ruɗani da ake ta cece-kuce kan makarantar.
Iyalan yarinyar sun ce an ba su bayanai mabambanta kan musabbabin mutuwar Nihal. Yayin da makarantar ta ce ta rasu ne sakamakon tashin ciwon cutar asma, wasu bayanai sun nuna cewa an hukunta ta ne saboda jinkirin zuwa masallaci, inda ake zargin manyan ɗalibai mata sun yi mata bulala tare da tilasta mata yin durƙushe na tsawon lokaci kafin ta faɗi ta suma.
Mahaifiyarta, Nusaiba Rabiu Dan Sheriff, ta ce an kira iyalinsu zuwa asibiti inda aka tabbatar musu da mutuwar yarinyar. Ta bayyana cewa ma’aikatan asibitin sun tambaye su ko Nihal na fama da cutar asma, lamarin da ya ƙara jefa su cikin shakku. Ta kuma ce ta lura da wasu alamomi a jikin gawar ɗiyarta da suka sa ta fara tambayar ko an ɓoye mata wani abu game da abin da ya faru.
Ta ce tana da yaƙinin akwai wasu bayanai da har yanzu ba a bayyana ba, saboda haka ta buƙaci gwamnati da hukumomin da abin ya shafa su gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar lamarin da kuma hukunta duk wanda aka samu da hannu a mutuwar yarinyar.
Da aka tuntuɓi shugabar makarantar, Reverend Sister Christiana Diyab, ta ce ba za ta yi magana kan lamarin ba a yanzu saboda yana hannun ‘yansanda. A nata ɓangaren, Rundunar ‘Yansandan Kano ta tabbatar da kafa kwamitin bincike na musamman bayan karɓar ƙorafi daga iyalan marigayiyar.
Daily Trust ta rawaito cewa, rundunar ta ce ta gayyaci malamai uku, manyan ɗalibai mata uku da wasu shaidu biyu domin bayar da bayani, yayin da ake ci gaba da gwaje-gwajen likitanci da na kimiyyar bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwar Nihal.















Discussion about this post