Wani ruwan sama mai ƙarfi da ya zo tare da iska mai ƙarfi ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da lalata gidaje da kadarori da dama a ƙauyen Bara da ke ƙaramar hukumar Kirfi ta jihar Bauchi.
An bayyana waɗanda suka rasu da Aisha Sagir mai shekaru 50 da kuma jikarta Aisha Shuaibu mai shekaru 4, duk mazauna Unguwar Katsinawa da ke ƙauyen Bara.
Rundunar ’yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar ranar Laraba.
A cewar sanarwar, mummunan lamarin ya faru ne ranar Talata bayan wani mamakon ruwan sama da ya zo tare da iska mai ƙarfi, wanda ya haddasa asarar rayuka da kuma lalacewar dukiyoyi a yankin.















Discussion about this post