ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

by Sulaiman and CGTN Hausa
54 minutes ago
Sin

Yayin da gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya ta 2026 ke karantowa, birnin Yiwu na kasar Sin, wanda a kan kira da “Cibiyar cinikayyar kananan kayayyaki ta duniya”, a yanzu ya kara cika da hada-hada. ‘Yan kasuwar birnin sun yi hasashen karuwar adadin odar kayayyakinsu masu nasaba da gasar ta cin kofin duniya ta bana, da kaso 20 zuwa 30 bisa dari idan an kwatanta da na shekarun baya. Wannan kuma manuniya ce dake haska karsashin fannin cinikayyar waje na kasar.

Wasu alkaluma da gwamnatin Sin ta fitar a jiya Talata, sun nuna yadda darajar adadin hada-hadar hajojin shige da fice na Sin, cikin watanni biyar na farkon bana ya kai yuan tiriliyan 20.68, wanda ya nuna karuwar kaso 15.3 bisa dari a mizanin shekara-shekara.

Kazalika, tun daga farkon shekarar ta bana, kasar Sin ta ci gajiyar cikakken fifikonta, a fannoni irinsu cikakken tsarin ayyukan masana’antu, da na kasuwa mai fadi, da yadda ta ingiza ci gaban hada-hadar shige da ficen hajoji bisa daidaito.

ADVERTISEMENT

A yanzu haka, kasar Sin ba kawai ta shirya zama “Masana’antar duniya” kadai ba ne, har ma ta shirya zama “Kasuwar duniya”, inda a cikin watanni biyar na farkon bana, kasar ta bunkasa shigo da hajoji da kaso 20.5 bisa dari kan mizanin shekara-shekara, adadin da ya haura daukacin bunkasar hada-hadar shige da fice.

Wani abun lura ma shi ne tun daga ranar daya ga watan Mayun da ya gabata, Sin ta aiwatar da cikakkiyar manufar nan ta kawar da haraji kan hajojin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, matakin da kai tsaye ya bunkasa cinikayya tsakaninta da kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Ko shakka babu manufar kasar Sin ta bunkasa ci gaba bisa daidaito a fannin shige da ficen hajoji na kara zama aiki na hakika. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja
  • Sulaiman
    Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
  • Sulaiman
    Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

MASU ALAKA

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Next Post
An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.