Yayin da gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya ta 2026 ke karantowa, birnin Yiwu na kasar Sin, wanda a kan kira da “Cibiyar cinikayyar kananan kayayyaki ta duniya”, a yanzu ya kara cika da hada-hada. ‘Yan kasuwar birnin sun yi hasashen karuwar adadin odar kayayyakinsu masu nasaba da gasar ta cin kofin duniya ta bana, da kaso 20 zuwa 30 bisa dari idan an kwatanta da na shekarun baya. Wannan kuma manuniya ce dake haska karsashin fannin cinikayyar waje na kasar.
Wasu alkaluma da gwamnatin Sin ta fitar a jiya Talata, sun nuna yadda darajar adadin hada-hadar hajojin shige da fice na Sin, cikin watanni biyar na farkon bana ya kai yuan tiriliyan 20.68, wanda ya nuna karuwar kaso 15.3 bisa dari a mizanin shekara-shekara.
Kazalika, tun daga farkon shekarar ta bana, kasar Sin ta ci gajiyar cikakken fifikonta, a fannoni irinsu cikakken tsarin ayyukan masana’antu, da na kasuwa mai fadi, da yadda ta ingiza ci gaban hada-hadar shige da ficen hajoji bisa daidaito.
A yanzu haka, kasar Sin ba kawai ta shirya zama “Masana’antar duniya” kadai ba ne, har ma ta shirya zama “Kasuwar duniya”, inda a cikin watanni biyar na farkon bana, kasar ta bunkasa shigo da hajoji da kaso 20.5 bisa dari kan mizanin shekara-shekara, adadin da ya haura daukacin bunkasar hada-hadar shige da fice.
Wani abun lura ma shi ne tun daga ranar daya ga watan Mayun da ya gabata, Sin ta aiwatar da cikakkiyar manufar nan ta kawar da haraji kan hajojin kasashen Afirka 53 da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, matakin da kai tsaye ya bunkasa cinikayya tsakaninta da kasashen Afirka.
Ko shakka babu manufar kasar Sin ta bunkasa ci gaba bisa daidaito a fannin shige da ficen hajoji na kara zama aiki na hakika. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post