Shugaban kungiyar masu masana’antu ta kasar Zambia Mohammed Umar, ya ce manufar kasar Sin ta kawar da daukacin harajin kwastam kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa kasar Sin, za ta samar da dama ta bunkasa ci gaban masana’antun dake kasashen Afirka da fadada zuba jari a fannin kere-keren nahiyar.
Umar, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta baya bayan nan da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, ya ce “Muna maraba da wannan mataki. Muna jinjinawa gwamnatin Sin bisa samar da manufa mai tallafawa ci gaban masana’antun Afirka. Da wannan mataki, Afirka za ta samu karin dama ta yin gogayya a fannin fitar da hajoji zuwa kasar Sin.”
Dan kasuwar ya kuma ce manufar wadda ta fara aiki tun daga ranar daya ga watan nan na Mayu, ta samar da karin sauki ga masu masana’antu, a kokarinsu na fadada sarrafa hajoji, ta yadda za su samu zarafin shiga babbar kasuwar kasar Sin.
Umar ya kara da cewa, ana sa ran wannan manufa za ta fadada janyo jarin waje, ciki har da jari daga wajen nahiyar, da sashen ayyukan masana’antu ta yadda za su ci gajiya daga karuwar fitar da hajoji zuwa Sin karkashin tsarin janye harajin kwastam na gwamnatin kasar. Daga nan sai ya bayyana kyakkyawan fatan cewa, manufar za ta ingiza ci gaban masana’antun Afirka baki daya. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post