Babban daraktan cibiyar bunkasa cinikayya da harkokin masana’antu ta birnin Abuja fadar mulkin tarayyar Najeriya ko ACCI Agabaidu Jideani, ya ce matakin kasar Sin na kawar da daukacin harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa Sin, zai amfani ‘yan kasuwar Najeriya dake fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin Sin, tare da taimakawa wajen karfafa dangantakar cinikayya tsakanin kasashen biyu.
Agabaidu Jideani, wanda ya bayyana hakan a jiya Lahadi yayin zantawarsa da manema labarai, ya ce manufar wadda aka fara aiwatarwa tun daga ranar daya ga watan nan na Mayu, za ta ingiza ci gaban sassa kamar na noma, da na sarrafa albarkatun gona, da fannin ma’adanai, da kananan masana’antu.
A daya hannun, karin damar shiga kasuwa zai kyautata damar gogayyar hajojin Najeriya a kasar Sin.Bugu da kari, Jideani ya ce amfani da wannan manufa yadda ya kamata zai taimakawa kokarin da ake yi na fadada fannin fitar da hajojin Najeriya, da bunkasa samar da kudaden musaya na waje.
Daga nan sai ya yi kira ga masu fitar da hajoji na kasar da su himmatu wajen cika ka’idojin kasuwa na Sin dangane da ingancin kaya, da yanayin kunshi da tafiyar da oda yadda ya kamata, kana ya bukaci gwamnatin Najeriya da ta tallafa wajen inganta takarar hajojin kasar. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post