Tsohon shugaban Hukumar Ilimi ta Bai Ɗaya ta jihar Neja (SUBEB) kuma jigo a jam’iyyar APC, Mohammed Bawa Niworo, ya samu ‘yanci bayan shafe watanni takwas a hannun ‘yan bindiga.
Rahotanni sun bayyana cewa an sake shi ne bayan iyalansa sun biya ƙarin kuɗin fansa naira miliyan 50, baya ga naira miliyan 30 da suka biya tun a watan Disambar bara bayan an sace shi a tsakiyar watan Satumban 2025.
An ce tun farko ‘yan bindigar sun nemi naira miliyan 150 domin sakinsa bayan sun yi garkuwa da shi a hanyar New Bussa zuwa Mokwa kusa da yankin Ibrahim Badamasi Babangida University da ke ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Neja.
Wani ɗan uwa da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun sake tuntuɓar iyalan makon da ya gabata suna barazanar kashe shi saboda rashin lafiya da yake fama da ita idan ba a biya ƙarin kuɗin ba. “Mun haɗa kuɗin muka biya jiya, sannan suka sake shi da misalin ƙarfe 6 na yamma,” in ji majiyar.
Ana sa ran ƙarin bayani kan lamarin nan gaba kaɗan.















Discussion about this post