ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Soke Harajin Kwastam Ga Kasashen Afirka Za Ta Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Bangarorin Biyu

by Sulaiman
1 month ago
Sin

Shekarar bana ita ce ta cika shekaru 70 da fara kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, kuma shekara ta farko ta aiwatar da shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15. A cikin wannan shekara ta musamman, wata yarjejeniya game da harajin kwastam ta zo a kan lokaci kamar yadda aka zata.

Daga yau Juma’a, wato 1 ga watan Mayu, Sin ta fara soke harajin kwastam na tsawon shekaru biyu ga kasashe 20 na Afirka da ke da dangantakar diflomasiyya da ita, wadanda ba su cikin kasashe mafi karancin ci gaba. Ta haka ne za a cimma burin soke harajin kwastam ga dukkannin kasashe 53 na Afirka masu dangantaka da Sin.

To, mene ne manufar ta soke harajin kwastam za ta kawo wa Afirka?Da farko, wannan mataki yana ba wa Afirka kariya don fuskantar kalubale da hadurra.

ADVERTISEMENT

A halin yanzu, ana kara samun tabarbarewar yanayin siyasa a duk duniya, yayin da ra’ayin ba da kariyar ciniki da na bangaranci ke karuwa.

Saboda haka, kasashen Afirka suna bukatar gaggauta fadada fitar da kayayyaki zuwa ketare da jawo jari daga waje, domin kawar da matsalolin da ke dakile ci gabansu.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Yadda kasar Sin ta soke harajin kwastam ga Afirka a dukkan fannoni ba tare da gindaya wani sharadi na siyasa ba, babu shakka yana ba wa kayayyakin Afirka damar shiga kasuwa mafi girma, kuma yana karfafa gwiwar kasashen Afirka wajen tabbatar da ci gaban tattalin arzikinsu.

Baya ga haka kuma, manufar za ta gaggauta ci gaban kasashen Afirka, duba da cewa hakan zai jawo karin jarin waje zuwa Afirka, baya ga fasahohi da ma kwarewar gudanarwa, wanda hakan zai taimaka wajen sarrafa kayayyaki a kasashen Afirka, sannan a fitar da su zuwa Sin.

Hakan kuma zai taimaka wa Afirka wajen bunkasa masana’antu da zamanantar da aikin gona, ta yadda Afirka za ta rike ragamar ci gaba a hannunta sosai.

Wannan “takardar izini” ta soke harajin kwastam, ba wai kawai ta bude sabon shafi na hadin gwiwar Sin da Afirka ba ne, har ma ta kara wa tattalin arzikin duniya kwarin gwiwa da kuma karfin kuzari, sannan ta sa al’ummar duniya sun fahimci cewa, bude kofa, da hakuri da juna, da samun ci gaba tare, su ne hanya madaidaiciya. (Bilkisu Xin)

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

Shugaban ADC Tsagin Nafiu Bala Ya Fice Daga Jam’iyyar, Ana Hasashen Zai Koma APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.