Shugaban jam’iyyar ADC tsagin Nafiu Bala Gombe, Honorabul Leke Abejide, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar.
Ɗan majalisar mai wakiltar mazaɓar Yagba ta tarayya a Jihar Kogi ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja ranar Juma’a.
Abejide ya danganta matakin da ya ɗauka da rikicin shugabanci da ya daɗe yana addabar jam’iyyar da kuma matsalolin shari’a da ka iya hana ta tsayar da ‘yan takara a babban zaɓen 2027.
Ko da yake bai bayyana jam’iyyar da yake shirin komawa ba kai tsaye, irin hular da ya sanya — wadda ake dangantawa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, jagoran APC — ta nuna yiwuwar komawarsa jam’iyyar mai mulki.
Abejide ya kuma sanar da cewa ya miƙa tsarin jam’iyyar ADC ga Nafiu Bala Gombe.















Discussion about this post