Babban manajan kungiyar masu fitar da kofi daga kasar Habasha Gizat Worku, ya bayyana a jiya Talata cewa, masu fitar da kofi na Habasha, sun fara cin gajiyar manufar kasar Sin ta sokewa kasashen nahiyar Afirka daukacin harajin kwastam, don fadada fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwar Sin.
Cikin ’yan kwanakin baya ma, Worku ya taba shaida wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, Sin ta soke haraji kan kofin kasar Habasha tun shekaru biyu da suka gabata, wanda hakan ya sa yawan kofi da ake fitarwa zuwa kasar Sin a duk shekara ke karuwa, daga kimanin tan 2,000 a shekaru biyar da suka gabata, zuwa tan 36,000 a shekarar da ta gabata.
Worku, ya kuma yaba da alkawarin gwamnatin Sin na tallafa wa kasashen Afirka, yana mai cewa, wannan manufa “hanya ce mai amfani ga bangarorin biyu”, wadda za ta haifar da fa’ida ta dogon lokaci ga al’ummar Sin da Afirka.
Babban manajan ya bayyana cewa, idan aka yi la’akari da karuwar bukatu cikin sauri, musamman ga kofi na musamman, Sin za ta zama babbar kasuwar kofi ga kasar Habasha a cikin shekaru uku masu zuwa. (Amina Xu)














Discussion about this post