An gudanar da wani taron kara wa juna sani game da manufar soke haraji ta kasar Sin ga kasashen Afrika 53 masu huldar diplomasiyya da ita, a birnin Abujan Nijeriya a karshen mako, wanda ya samu halartar jakadan Sin a Nijeriya da karamin ministan kula da cinikayya da sauran manyan jami’ai na kasar. Har kullum, idan masana suna zancen bunkasa tattalin arziki a Nijeriya, su kan yi jan hankali kan kasar ta yi hobbasa ta rika fitar da kayayyaki ketare domin bunkasa harkokin masana’antu a cikin gida da samar da aikin yi da karfafa tattalin arzikinta. Ba Nijeriya ba, kusan dukkan kasashen Afrika ne suke dogaro da shigar da kayayyaki maimakon fitar da su.
A ganina, manufar ta kasar Sin ta tabbatar da burin da aka dade ana son gani, watau kasashen nahiyar Afrika su zama masu sarrafa kayayyaki da albarkatun da suke da shi domin karfafa tattalin arzikinsu da dogaro da karfinsu da kyautata rayuwar jama’a. Wannan manufa ta farkar da kasashen Afrika da karfafa musu gwiwar cin ribar albarkatun da suke da shi yadda ya kamata, lamarin da zai bunkasa samar da aikin yi da ma kwarewa a kasashen.
Uwa uba, manufa ce da ke nuna burin kasar Sin na ganin kasashen Afrika sun zama masu tsayawa da kafafunsu maimakon masu jira a taimaka musu. Rahotanni sun ruwaito cewa, tun bayan fara aiwatar da manufar a ranar 1 ga watan Mayun bana, an samu habakar fitar da kayayyaki daga Nijeriya zuwa kasar Sin inda darajar cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta kai dala biliyan 18. Kana yawan kayayyakin da ake fitarwa daga Nijeriya zuwa Sin ya karu da kaso 80 zuwa dala biliyan 2.3, inda karuwar da ake samu a kowane wata ya zarce kaso 40 a watan Mayu da Yuni. Irin wannan kyakkyawar dangantaka da Sin, ita ce ainihin hadin gwiwar da ya kamata a rika gani tsakanin kasashen duniya, inda za a rika samun moriyar juna da tallafawa marasa karfi ta yadda za su tsaya da kafafunsu, ba wai tallafi mai sharadi da zai mayar da su karkashin ikon wata kasa ba.
Tasirin wannan manufa ba zai misaltu ba, domin idan kasashen Afrika suka yi amfani da ita yadda ya kamata, abu ne da zai kara inganta hadin kansu da dunkulewarsu guri guda musammam bisa la’akari da yarjejeniyar cinikayya cikin ’yanci ta Afrika da ke akwai a tsakaninsu.
Har ila yau, ta zama kyakkyawan misali dake adawa da kariyar cinikayya tare da bude kofar karfafa cinikayya mai adalci tsakanin kasa da kasa ba tare da gindaya sharudda ba, da kuma karfafa hadin kan kasashe masu tasowa. (Fa’iza Mustapha)














