Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa raguwar farashin kayan abinci da ake gani a kasuwanni a ‘yan kwanakin nan, na da nasaba da manufofi da matakan musamman da aka ɗauka domin gyara harkar kasuwa da ƙarfafa samar da abinci a cikin gida.
Ministan Noma da samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a yayin taron majalisar noma ta ƙasa karo na 47 da aka gudanar a Kaduna, ranar Alhamis 6 ga Nuwamba, 2025.
A cewar ministan, gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki alƙawarin tabbatar da ikon cin gashin kai a fannin abinci, inda Nijeriya za ta riƙa samar da abincin da ta ke ci, tare da tabbatar da wadatar kayayyaki a farashi mai sauƙi.
Kyari ya bayyana cewa shirin National Agricultural Growth Scheme–Agro-Pocket (NAGS–AP), wanda ake aiwatarwa tare da hadin gwiwar Babban Bankin Raya Afirka (AfDB) da jihohi, shi ne ginshikin inganta samar da kayayyakin noman da kuma bunkasa amfanin gona.















Discussion about this post