Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya sanar da gudanar da wasu harkokin diflomasiyya a yau Litinin, inda ya bayyana cewa, ziyarar shugaban kasar Pakistan Asif Ali Zardari a kasar Sin na gudana ce daga ranar 25 ga watan Afrilu zuwa 1 ga watan Mayu, kuma ta kunshi zuwa lardin Hunan da lardin Hainan.
Lin ya kara da cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasar Pakistan wajen karfafa mu’amalar sada zumunta da hadin gwiwa a dukkan matakai da yankuna daban-daban, tare da hada karfi da karfe wajen gina al’ummar Sin da Pakistan mai alaka ta kut-da-kut da kuma kyakkyawar makoma ta bai-daya.
Har ila yau, bisa gayyatar da ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya yi masa, mataimakin firaminista kuma ministan harkokin wajen Belgium, Maxime Prevot, yana kan ziyarar aiki ta farko a kasar Sin tun bayan rantsar da shi a kujerarsa, daga ranar 27 ga watan Afrilu zuwa 1 ga watan Mayu.
Bugu da kari, ita ma ministar harkokin wajen Australia, Penny Wong, za ta ziyarci kasar Sin daga ranar 28 zuwa 30 ga watan Afrilu. A yayin ziyararta, ita da ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi za su jagoranci taron shawarwarin diflomasiyya da manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Australia karo na takwas. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post