Akalla mutane 11 ne aka ruwaito sun mutu a wani sabon harin ‘yan bindiga da suka kai ƙauyen Gurbi da ke ƙaramar hukumar Kankara a Jihar Katsina da yammacin ranar Lahadi.
Da yake tabbatar da harin, kakakin rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq, ya bayyana a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai ranar Litinin a Katsina cewa, harin da maharan suka kai ƙauyen Gurbi da misalin ƙarfe 2:40 na rana ya kuma jikkata mutane biyu.
Sanarwar ta ce: “Rundunar ‘Yansandan Jihar Katsina tana sanar da jama’a cikin alhini game da harin ‘yan bindiga da aka kai ƙauyen Gurbi, ƙaramar hukumar Kankara, Jihar Katsina, wanda ya faru da misalin ƙarfe 2:40 na rana a ranar 26 ga Afrilu, 2026.
“Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari ƙauyen inda suka harbe mutane 11 har lahira, yayin da wasu biyu suka samu raunuka daban-daban kafin isowar jami’an tsaro.”
Sanarwar ta ƙara da cewa bayan samun kiran gaggawa, tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa da ta haɗa da ‘yansanda, sojoji da sauran hukumomin tsaro ƙarƙashin jagorancin DPO ta garzaya wurin da lamarin ya faru. Maharan sun tsere bayan sun hangi jami’an tsaron suna tunkararsu.















Discussion about this post