Bisa gayyatar shugaban kasar Guinea Mamady Doumbouya, manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, Zheng Jianbang, ya halarci bikin rantsuwar kama aiki na shugaba Mamady Doumbouya, da ya gudana a birnin Conakry na kasar Guinea a ranar 17 ga wata, inda kuma shugaba Doumbouya ya zanta da Mista Zheng.
Yayin zantawar, Mista Zheng ya mika ma shugaba Mamady Doumbouya gaisuwa da fatan alheri daga shugaba Xi Jinping na kasar Sin, kana ya ce kasar Sin na dora matukar muhimmanci kan huldar dake tsakanin kasashen 2, tana kuma son aiki tare da kasar Guinea wajen karfafa zumunta, da zurfafa hadin gwiwa mai tabbatar da moriyar juna, da daga huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare ta kasashen 2 zuwa wani sabon mataki.
A nasa bangare, shugaba Doumbouya ya bukaci Zheng da ya mika gaisuwa da godiyarsa ga shugaba Xi Jinping. Ban da haka, shugaban ya ce kasar Guinea tana daukar abokantakar dake tsakaninta da kasar Sin da daraja, kuma tana son zurfafa hadin gwiwa a bangarori daban daban, da kara kyautata hulda da kasar Sin. (Bello Wang)















Discussion about this post