Ƙasar Senegal ta lashe gasar cin kofin ƙasashen Afrika ta shekarar 2025 bayan ta doke mai masaukin baƙi, Morocco, da ci 1-0 a wasan ƙarshe da aka buga a filin wasa na Prince Moulay Abdellah da ke birnin Rabat.
Wannan ita ce gasar AFCON ta 35 da aka gudanar a tarihi. Bayan kammala wasannin, an raba kyaututtuka da dama da suka haɗa da zakarun gasar, da gwarzon ɗan wasa, wanda ya fi zura kwallo, da kuma gwarzon mai tsaron raga.
- AFCON 2025: Muhimman Abubuwa Da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Karshe Tsakanin Senegal Da Morocco
- AFCON 2025: Nijeriya Ta Kare A Matsayi Na Uku Bayan Doke Masar
Jerin Wadanda Suka Lashe Kyaututtuka:
Zakarun Gasar: Senegal
Matsayi na Biyu: Morocco
Matsayi na Uku: Nijeriya
Kasar da Tafi Son Zaman Lafiya: Morocco
Gwarzon Dan Wasan Gasar: Sadio Mané (Senegal)
Gwarzon Mai Tsaron Raga: Yassine Bounou (Morocco)
Wanda Ya Fi Kowa Zura Kwallo: Brahim Díaz (Morocco) – Ƙwallaye 5 a wasanni 7
Gasar AFCON ta 2025 za ta kasance cikin gasannin da za a daɗe ana tunawa da su, sakamakon gagarumar fafatawa, da jajircewar da sadaukarwa daga dukkanin ƙasashen da suka halarta.
Musamman wasan ƙarshe, wanda aka shafe mintuna masu cike da zarya da kai komo, ciki har da bugun daga kai sai mai tsaron raga kafin tashi daga wasan, wanda ya bai wa Morocco damar shiga gaba, amma ta ɓarar. Senegal ta tsaya daram har ta lashe kofin daga ƙarshe ta hanyar cin ƙwallo guda bayan ƙarin lokaci.















Discussion about this post