Wani masani mai fashin baki kan tattalin arziki a kasar Ghana Jonas Atingdui ya bayyana cewa, manufar soke harajin kwastam ta kasar Sin ga kasashen Afirka 53 da za ta fara aiki a ranar 1 ga watan Mayu mai zuwa, wani mataki ne mai kawo sauyi na ci gaba, kuma kuzari mai karfafa bunkasar tsarin sarrafa kayayyakin aikin gona da ma’adanai da masana’antu, tare da kara habaka cinikayya a cikin nahiyar.
Atingdui ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a wata hira da ya yi da shi a baya-bayan nan cewa, babbar damar da aka samu ta cin gajiyar kasuwar kasar Sin mai yawan al’umma biliyan 1.4 zai amfanar da masu fitar da kayayyakin amfanin gona irin su koko, mankade, katako da ma’adanai, musamman kayayyakin da aka sarrafa a masana’antu.
Ya kara da cewa, “Manufar soke haraji ta kasar Sin ga daukacin kasashen Afirka 53, wani lamari ne mai kawo sauyi na ci gaba, kuma mai muhimmanci ta bangarori da dama. Yayin da kasar Amurka ke kara rufe kasuwanninta ga duka kasashen Afirka da kawayenta, matakin da kasar Sin ta dauka na soke biyan harajin kwastam yana samar da wata kasuwa ta daban don cike gibin da hasarar kudaden waje daga Amurka ta haifar.”
Bugu da kari, ya yi kira da a karfafa ka’idojin inganta kayayyaki, yana mai gargadin cewa, kayayyaki marasa inganci daga kasashen Afirka na iya kawo cikas ga dorewar samun shiga kasuwar kasar Sin. Sai dai kuma ya ce, “Fahimtar ka’idojin inganta kayayyaki na kasar Sin a zahiri za ta habaka tabbatar da inganci, da ilimi da hanyoyin sarrafa kaya.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post