Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi zargin cewa akwai wani shiri na hana jam’iyyar ADC shiga zaɓen 2027. Ya ce ya samu sahihan bayanai da ke nuna cewa ana ƙoƙarin amfani da hanyoyin siyasa da na shari’a domin cire jam’iyyar daga takarar zaɓe.
Atiku ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar. Wannan na zuwa ne bayan tsohon Mataimakin Sakataren Yaɗa Labarai na APC, Timi Frank, shi ma ya yi irin wannan zargi kan wata maƙarƙashiya da ya ce ta shafi Fadar Shugaban Ƙasa, da INEC da wasu ɓangarori na shari’a.
Atiku ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su tashi tsaye wajen kare dimokuraɗiyya, yana mai cewa babu wata gwamnati da ke da ikon hana jama’a zaɓar jam’iyyar da suke so. Ya ƙara da cewa idan APC tana da tabbacin farin jininta, bai kamata ta ji tsoron ADC ba.
Ya kuma yi kira ga alƙalai, da INEC, da hukumomin tsaro da ƙungiyoyin fararen hula su kasance cikin shiri domin kare sahihancin zaɓe. A cewarsa, amfani da cibiyoyin gwamnati ko kotuna wajen murƙushe adawa barazana ce ga dimokuraɗiyya.
Atiku ya jaddada cewa babu wata barazana ko matsin lamba da za su hana miliyoyin ‘yan Nijeriya ci gaba da goyon bayan ADC, yana mai cewa burin sauyi ba za a iya dakatar da shi ba kuma ƙudurin al’umma zai yi nasara.














