Jam’iyyar ADC ta bayyana aniyarta ta kwace mulki a Jihar Borno da ma matakin kasa baki daya a zaben 2027, tana danganta karuwar hare-haren tsaro da gazawar shugabanci a matakan jiha da tarayya.
Shugaban jam’iyyar a Borno, Kolo Bukar, ya bayyana hakan ne bayan rantsar da sabbin shugabannin jam’iyyar a Maiduguri, inda ya ce duk da ƙalubalen da jam’iyyar ke fuskanta, za ta shawo kansu tare da samun nasara.
- Rikicin Cikin Gida: ADC DA PRP An Fara Zawarci
- Kabiru Marafa Ya Jagoranci Daruruwan Mabiyansa Zuwa ADC A Zamfara
Bukar ya zargi jam’iyyar mai mulki APC da gaza magance matsalolin tsaro da talauci, yana mai cewa ADC za ta kawo sauyi mai ma’ana da ingantaccen shugabanci idan ta samu dama.
Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar na shirya tsare-tsare na musamman domin daƙile matsalar tsaro a Borno da sauran sassan ƙasar, tare da tabbatar da walwalar al’umma.
A nasa ɓangaren, jigon jam’iyyar a jihar, Alhaji Kashim Imam Matawalle, ya ce burinsu ba kawai ƙwace mulki ba ne, har ma da kawo ƙarshen wahalhalun talakawa, yana mai sukar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu kan yadda take tafiyar da harkokin ƙasa.















Discussion about this post