ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu NYSC Ne Kadai Za Su Kula Da Na’urar Tantance Katin Zabe – INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa matasa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) ne kaɗai ta bai wa iznin riƙa amfani da na’urar BVAS domin tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe gangariya.

 

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyara cibiyar horas da Jami’an Zaɓe da Mataimakan Jami’an Zaɓe na I da na II, ranar Asabar, a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • INEC Na Sa Ran Karbar Sauran Kudaden Sallamar Ma’aikatanta Daga CBN Yau Talata – Okoye

Yakubu ya ce INEC ba ta da isassun ma’aikatan da za su iya gudanar da zaɓe a faɗin ƙasar nan kuma a lokaci guda. Ya ce dalili kenan ta ke ɗaukar masu yi wa ƙasa hidima domin samar da sahihi kuma kuma karɓaɓben zaɓe ba tare da tashin hankula ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Shugaban ya gargaɗi matasan NYSC su nuna kishin Nijeriya da ‘yan Nijeriya, ba kishin wata jam’iyya ba.

 

Farfesa Yakubu ya kuma gargaɗi matasan cewa kada su yi kuskuren bai wa wani ajiya, tsaro ko kulawar na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS a hannun wani can daban.

 

Haka kuma ya ce kowane ɗan bautar ƙasa mai amfani da BVAS za a riƙa bibiyar sa ta lambar bibiyar ƙwaƙwaf, wato ‘code’ ko ‘tracker’.

 

Ya ce, “Nijeriya ta yi sa’a da gamo-da-katarin samun matasa irin ku. Saboda babu yadda INEC za ta iya shirya zabe ba tare da gagarimar gudummawar ku ba.

 

“Saboda haka mun dogara a kan ku da sauran ma’aikata. Amma ku ne za ku fi saura gudanar da aikin zaɓe mafi muhimmanci a rumfunan zaɓe. Saboda a can ne jama’a za su je su yi zaɓe. Kuma kowanen ku zai yi rantsuwar cewa ba zai goyi bayan kowace jam’iyyya ba.

 

“Kishin ku ya tsaya kan Nijeriya da ‘yan Nijeriya kaɗai, ba kan jam’iyya ba. Ku kasance ku ne tamkar shugabannin INEC a rumfunan zaɓen ku. Ku ne ma sarakunan daulolin rumfunan zaɓe.

 

“Ku kaɗai ne aka bai wa iznin sarrafa na’urar BVAS a ranar zaɓe. Don haka ku ɗauki wannan aiki da muhimmanci.”

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Takwaransa Na Zambiya

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Takwaransa Na Zambiya

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.