A baya-bayan nan, Japan tana ta aiwatar da wasu matakai na takalar fada da kokarin mayar da hannun agogo baya dangane da nasarar da aka samu cikin lokaci mai tsawo, wanda nake ganin ganganci ne ko wasa da wuta.
Shin rashin sanin tarihi ne ko kuma rashin girmama tarihi da nasarar da aka samu ne ke ingiza Japan?
Duk wanda ya san yanayin tafiyar da huldar diplomasiyya, ya san cewa, kowace kasa na da inda ta ja layi. Don haka, kowa ya san cewa, batun Taiwan, wani batu ne da Sin ta sha jan kunne a kai, kuma sanin kowa ne, yankin Taiwan wani bangare na Sin da take nanata cewa, babu wanda zai iya balle shi, kuma ba makawa kasar za ta cimma burinta na dunkule dukkan yankunanta wuri guda.
Radadi da wahalhalu da asarar da aka yi sakamakon yakin duniya na biyu, abu ne da ya kamata ya zama izina da darasi ga kasa da kasa, ciki har da Japan. Kana nasarar da aka samu bayan yakin, muhimmin abu ne da ya kamata a girmama kuma a daukaka. Japan ta mika wuya ba tare da sharadi ba, kuma ta amince da Sanarwar Potsdam, inda ta yi alkawarin za ta cika dukkan ka’idojin da sanarwar ta zayyana, kuma ta mayar da yankin Taiwan ga Sin ba tare da wani sharadi ba. Amma kalaman da aka ji sabuwar firaministar kasar na furtawa, da ma wasu ’yan siyasar kasar, sun saba wa haka, har ma da dokokin MDD.
Shin Japan ba ta son girmama alkawarin da ta yi ne? Ko ba ta girmama sadaukarwar da magabata suka yi?
Har ila yau a baya-bayan nan, sojojin Japan sun yi ta kawo tsaiko ga atisayen sojojin kasar Sin da aka saba yi, a gabashin mashigar Miyako, bayan an riga an sanar da shirin atisayen tun kafin lokacin. Halin da Japan take nunawa a baya bayan nan, yunkuri ne na kawo tsaiko ga zaman lafiyar da ake mora a yankin, kuma bisa dukkan alamu, kokari take ta dawo da ra’ayin amfani da karfin soji. Sai dai, ya kamata ta gane cewa, duniya ta sauya, kuma munanan matakanta ba za su je ko ina ba, domin Sin na da karfin kare kanta.
Har kullum burin kasar Sin shi ne, wanzuwar tsaro a cikin gida da zaman lafiya da lumana da makwabtanta da shiyyarsu da ma duniya baki daya, ba don ba ta da karfin kare kanta ba, sai don ta fi ganin zaman lafiya a matsayin abun da zai amfanawa kowa, kuma shi ne muradin mafi rinjayen al’ummar duniya.













