Tsohon mataimakin shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka ta AU Erastus Mwencha, ya ce matakin kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026, ya dace da ajandar neman ci gaba ta AU, ta nan zuwa shekarar 2063.
Erastus Mwencha, wanda ya bayyana hakan a ranar Talata, ya ce nahiyar Afirka da kasar Sin, na da jimillar mutane kimanin biliyan 2.8, kuma sassan biyu suna da fahimtar juna a sassa da dama.
A daya bangaren kuma, nahiyar Afirka na da burin samar da ci gaba mai sanya jama’a gaban komai, ta hanyar bunkasa kwarewar sana’o’i tsakanin matasa ta hanyar hadin gwiwa da kasar Sin. Mista Erastus ya kara da cewa, tuni kasar Sin ta samar da dubban guraben karatu ga daliban kasashen Afirka, wanda hakan ya bunkasa damar nahiyar ta karbar ragamar ci gaban ta.
Ya ce nahiyar Afirka, za ta yi amfani da damar matasanta, ta hanyar aiki kafada da kafada da manyan cibiyoyin samar da horo, irin su cibiyar koyar da fasahohi ta Luban ta kasar Sin, a matsayin matakin da zai taimaka wajen rage ficewar kwararru daga nahiyar zuwa sauran sassan duniya.
A ranar takwas ga watan nan na Janairu ne aka kaddamar shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a, tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026 a helkwatar AU dake birnin Addis Ababan kasar Habasha. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post