• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mazan Yanzu Ba Sa Son Matan Da Za Su Zame Masu Jidali – Zahra

by Amina Bello Hamza
1 year ago
in Adon Gari
0
Mazan Yanzu Ba Sa Son Matan Da Za Su Zame Masu Jidali – Zahra
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zahra Muhammad da aka fi sani da Zahra Bentures, matashiyar ‘yar kasuwa ce a fannin fasahar zamani da kware wajen aika kayan kasuwarta ta hanyoyin intanet daba-daban, ta yi wa wakiliyar LEADERSHIP Hausa Amina Bello Hamza bayanin yadda yadda ta tsinci kanta a harkar kasuwanci da kuma yadda take tafiyar da shi. Sannan ta ja hankalin mata musamman masu aure kan su tashi su nemi na kansu, kada su dogara da abin da maigida zai rika basu, domin a cewarta su kansu mazan yanzun ba sa sanin matan da suke zame musu jidali a rayuwarsu ba, ga dai yadda ganawar tasu ta kasance.

Da Farko za mu so ki bayyana mana sunanki
Sunana Fatima Abdurrashid Muhammad, amma wasu sun fi sani na da Zahra Muhammad ko Zahra Bentures musamman a Facebook. Ina zaune a Garin Samaru Zariya, Kaduna. Ni daliba ce kuma ‘yar kasuwa mai tasowa. Na yi karatu tun daga matakin firamare har zuwa jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Ko malamar na da aure?
A a ba ni da aure

Wace sana’a kike yi a halin yanzu?

Ina gudanar da sana’a ta a karkashin kamfaninmu mai suna ZB Global Bentures, inda nake sayar da garin Danwake, yaji, da sauran abubuwan amfanin gida. ZB Data wani sashi ne na ZB Global Bentures in da muke saida Data, Airtime, Electricity Bill, Bulk SMS, Edam pin da sauran su. Muna da website (www.zbdata.com.ng) tare da application (zb Data) wanda mutum zai iya saukewa a play store domin ya fara sanar sayar da data, kati da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mene ne ya baki sha’awar fara wannan sana’a?

Gaskiya na ji dadin wannan tambayar sosai, wato ba komai bane ya sa na ji ina sha’awar sana’a ba illa son na ga burina ya cika. Don gaskiya ba wai na taso gidanmu na ga ana sana’a bane, ba ni mantawa lokacin da zan shiga jami’a takardu na bangaren kiwon lafiya na cika, a tunani na zan samu damar taimaka wa mutane a asibiti zan hadu da mutane daban-daban to sai dai Allah bai sa na samu ba, a nan ne na fara tunanin mafita, ta ya zan cimma burina, kawai sai na fara tunanin sana’a domin zan samu damar haduwa da mutane daban-daban, kuma zan tara kudin da zan iya taimaka wa al’umma. Amma akan hanyar na fahimci sana’a ta wuce yanda nake kallon ta na koyi abubuwa da daman gaske, na fahimci ba wai iya dan a tara kudi ko a hadu da mutane ba ake sana’a na kara samun dalilan da zai sa na ci gaba da sana’a ta domin ina jin dadin abin da nake tana kawo min kwanciyar hankali, debe kewa da jin dadi.

Idan mutum na son fara wannan sana’ar wane abu zai tanada don samun cikakkiyar nasara?

Eh to da farko dai kusan kowace sana’a ana bukatar jari, kamar kasuwancin data ko da Naira 2,000.00 mutum zai iya farawa, website da na fada a baya shi mutum zai zauna ya bude asusun, ko aje play store a sauke bayan shi kuma, mutum zai sa kudi a wallet shike nan sai ya fara sayarwa kwastomomi ana biyan sa, yana cin riba.

Wace shawara kike da shi ga al’umma?

Shawara ta ita ce duka maza da mata su tashi su nemi abin yi, yanayin ya canja musamman mata kar su zauna su nade hannu su ce komai sai an yi musu, don gaskiya idan ba su kai zuciya nesa ba sun ta ganin bacin rai, to abin duniyar ne ba isa yake ba, kuma su kan su mazan yanzun ba su san matan da za su zame masu jidali, akalla dai mace ta san dubarun nema na abin da ba’a rasa ba ya zama za ta iya daukewa kanta ba don ba za a iya yi mata ba, kuma akalla tana da dangi da za ta yi wa alheri ‘yan uwa da abokan arziki kin ga sai ta nema ne duk za ta iya wannan aikin ladan. Ya kamata a wurin nema mu dinga kallo da yin koyi da nana Khadija matar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama. Kuma ya zo cikin hadith cewa wajibi ne ga dukkan Musulmi ya nemi halal.

Menene burinki a wannan sana’ar taki?

Babban burina a sana’a ta shi ne na ga ya fadada ta hanyar samar wa Kowane nau’in mutum abin da ya fi dacewa da lafiyarsa wanda ya fi bukata, na samu na yi masa rijista da NAFDAC da sauran hukumomin da ya dace su sa hannu a kai, kuma na mallaki wurin da zan rika aje kayan hatsi kafin da bayan an sarrafa, na mallaki abin da zai saukaka min wurin zirga-zirga. Kuma nan gaba kadan ya zama har fitarwa waje za’a iya yi na kayanmu, na samu abubuwa mafi kyau da inganci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Man City Da Arsenal: Yadda Aka Yi Faɗuwar Guzuma A Wasan Da Aka Kece Raini A Etihad Etihad

Next Post

Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

2 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

3 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

6 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

7 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

7 months ago
Next Post
Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.