Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, ya yaba da matakin Sin na soke haraji baki daya ga kasashen Afrika, yana mai kira ga dukkan manyan kasashe da kasashe masu karfin tattalin arziki su yi koyi da matakin.
Da yake jawabi ga manema labarai a gefen taron AU na 39 a Addis Ababa, babban birnin Habasha, sakatare janar din ya nanata matsayinsa na adawa da shingayen ciniki masu tsauri.
Da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya nemi jin ra’ayinsa game da alfanun manufar soke harajin ta Sin ga harkokin cinikayya da tattalin arzikin Afrika, ya jadadda cewa, nahiyar na matukar bukatar cinikayyar kayayyakinta cikin ‘yanci. Ya ce bai kamata a hukunta nahiyar dake fama da wahalhalun tattalin arziki da shingayen cinikayya da harajin da ba za su ba kayayyakinta damar shiga takara ba.
A ranar Asabar ne kasar Sin ta sanar da cewa za ta fara aiwatar da manufar ta soke haraji da kaso 100 bisa 100 ga kasashen Afrika 53 dake da huldar diflomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayun 2026.
A lokaci guda kuma, kasar Sin za ta ci gaba da tattaunawa da rattaba hannu kan yarjeniyoyin da suka shafi hadin gwiwar tattalin arziki domin samun ci gaba na bai daya da kuma fadada damar shigar kayayyakin Afrika kasar Sin ta hanyar inganta hanyar shigar kayayyakin da ba sa bukatar haraji da ma sauran matakan da za su saukaka matakin. (FMM)














Discussion about this post