• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Shirin Kasar Sin Dangane Da Batun Palasdinu Da Isra’ila Ya Samu Amincewar Duniya?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Shirin Kasar Sin Dangane Da Batun Palasdinu Da Isra’ila Ya Samu Amincewar Duniya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Dangane da jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a yayin taron musamman ta kafar bidiyo tsakanin shugabannin BRICS kan batun Palasdinu da Isra’ila a ranar 21 ga wata, jaridar Al Ahram ta kasar Masar ta ruwaito cewa, kasashen Larabawa da na Musulmi suna mayar da hankali kan yadda har kullum kasar Sin take yin adalci kan batun Palasdinu da Isra’ila, sun kuma yaba mata sosai. Ana fatan kasar Sin za ta kara taka rawa kan batun.

Palasdinu da Isra’ila sun dauki wata guda ko fiye da haka suna bude wuta tsakaninsu a wannan karo, inda mutanen kasashen 2 fiye da 15500 suka rasa rayukansu, ciki had da kananan yara fiye da 5800 a zirin Gaza. A wannan yanayi ne a cikin jawabinsa a yayin taron musamman, shugaba Xi ya yi kira ga bangarori masu rikicin su dakatar da tsagaita bude wuta a tsakaninsu nan take, a tabbatar da wucewar kayayyakin agajin jin kai ba tare da tangarda ba, a yi kokarin kaucewa tsanantar rikicin da bazuwar tasirinsa a sauran sassan duniya. Ya kuma jaddada cewa, babbar hanyar kawo karshen rikicin da yaki-ci-yaki-cinyewa tsakanin Palasdinu da Isra’ila ita ce kafa kasashe biyu. Matakai 3 da shugaba Xi ya gabatar, matakai ne da wajibi ne a dauka yanzu da kuma a dogon lokaci, wadanda suka nuna manufar daidaita batun na Palasdinu da Isra’ila yadda ya kamata.

Me ya sa shirin kasar Sin ya samu amincewar Palasdinu da Isra’ila da ma sauran kasashen duniya? Saboda jama’ar Sin na rungumar zaman lafiya da adawa tashin hankali. Har kullum suna bayyana ra’ayoyi da tafiyar da harkoki bisa adalci. Sabanin yadda Amurka take mara wa Isra’ila baya, kasar Sin ba ta nuna son kai kan batun na Palasdinu da Isra’ila, tana yin adalci tsakanin bangarorin 2. Ta yi matukar fatan za a dakatar da bude wuta a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, su yi zaman tare cikin lumana. Har kullum kasar Sin na rungumar gaskiya da adalci.(Tasallah Yuan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BRICSFOCACSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Ciwo Bashin Biliyan 100 Don Gudanar Da Ayyukan More Rayuwa – Gwamnan Bauchi

Next Post

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Kasar Jamus

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

3 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

4 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

5 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

6 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

7 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

17 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Kai Ziyara Saudiyya Da Guinea Bissau

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Kasar Jamus

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.