ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Zumunci A Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Yake Da Danko Matuka

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A kwanakin baya ta yanar gizo, shugaban kasar Equatorial Guinea, Mr. Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, wanda ya yi ziyarar aiki a birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, ya gana da wakilan malamai da dalibai na wata makarantar firamare da ke gundumar Jinping ta lardin Yunnan da ke kudu maso yammacin kasar Sin. 

To, amma ina dalilin ganawar? 

Ashe, a yayin ziyarar da shugaban ya kawo kasar Sin a watan Afrilun shekarar 2015, a madadin gwamnatin kasarsa ya sanar da samar da gudummawar kudi don a gyarawa, da fadada wata makarantar firamare da ke gundumar Jinping, don nuna godiya ga kasar Sin bisa yadda ta dade tana taimakawa kasarsa wajen tabbatar da bunkasuwa. Bayan shekara guda, an kammala gina wani gini mai bene biyar a makarantar, matakin da ya kyautata yanayin karatu ga yaran wurin. Don tunawa da dankon zumunci a tsakanin kasashen biyu kuma, an gyara sunan makarantar ya zama makarantar sada zumunta a tsakanin Sin da Equatorial Guinea. A cikin shekaru 9 da suka gabata, sama da yara 2000 sun kammala karatu a makarantar.

ADVERTISEMENT

A hakika, kasar Equatorial Guinea kasa ce mai tasowa wadda ba ta da wadata, amma a yayin da ita kanta ke bukatar taimako, sai ga shi ta samar da gudummawa ga kasar Sin, kuma wannan ba shi ne karon farko na hakan ba, duba da cewa tun a shekarar 2008 a yayin da mummunar girgizar kasa ta afkawa kasar Sin, kasar ta Equatorial Guinea ta samar da gudummawar kudin EURO miliyan biyu ga kasar Sin.

Tabbas abu ne da ya ratsa zukatanmu, kuma ba a rasa irin wadannan labarai da suka faru a tsakanin Sin da kasashen Afirka. To, amma me ya sa Sin da kasashen Afirka suke da zumunci mai danko kamar haka? 

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Lallai kasancewar kasar Sin kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kuma Afirka nahiya ce mafi yawan kasashe masu tasowa, bangarorin biyu sun fuskanci makamantan abubuwan da suka faru gare su a tarihi, suna kuma da buri kusan iri daya da suke neman cimmawa, hakan ya sa dankon zumunci a tsakaninsu ya yi ta karfafa, kuma suke hada kai da juna don tabbatar da makomarsu ta bai daya. Idan ba a manta ba, a shekarun 1960 zuwa na 1970, Sinawa sama da dubu 50 sun hada kai da al’ummar Afirka wajen gina hanyar dogo ta Tanzania da Zambia, inda suka zubar da gumi da jini, har ma suka sadaukar da rayukansu, layin dogon da ya zama alamar zumunci a tsakaninsu. A shekarar 1971 kuma, kasashen Afirka sun bai wa kasar Sin babban taimako wajen mayar da ita kan kujerarta a MDD, inda daga cikin kasashe 23 da suka gabatar da shawarar, 11 sun kasance kasashen Afirka, baya ga kuri’u 76 da aka kada na nuna amincewa, wadanda a cikinsu wasu 26 kasashen Afirka ne suka kada. Yayin da aka shiga sabon karnin da muke ciki, huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ma sai karfafa take ta yi. A shekarar 2000, bangarorin biyu sun kafa dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC a takaice, dandalin da ya zamanto muhimmin tsari na yin shawarwari, da kuma hadin gwiwa a tsakanin su cikin shekaru 24 da suka gabata, tare da samar da nasarorin a zo a gani.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping yana dora matukar muhimmanci a kan cudanyar Sin da kasashen Afirka, wanda bayan da aka zabe shi a matsayin shugaban kasar a shekarar 2013, da kuma sake zabarsa a shekarar 2018, ya kai ziyararsa ta farko a matsayin shugaban kasa duk a nahiyar Afirka. Baya ga haka, ya kuma gabatar da manufar da ya kamata a bi wajen hulda da kasashen Afirka, wato nuna sahihanci, da samar da hakikanin sakamako, da kauna da kuma rikon gaskiya, don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakaninsu.

A jawabin da ya gabatar a yayin ziyararsa a kasar Tanzania a shekarar 2013, ya ce, “kasar Sin ta samar da gudummawa ga kasashen Afirka gwargwadon karfinta, kuma godiya take ga kasashen Afirka, da ma al’ummarsu bisa ga goyon baya da ma taimako da suka dade suna ba ta. A kan batutuwan da suka shafi babbar moriyar juna, kullum matsayinmu a bayyane yake, wato muna tsayawa tsayin daka wajen goyon bayan juna.” Furucinsa ya bayyana ainihin zumunci dake tsakanin sassan Afrika da Sin. (Lubabatu)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
Daga Birnin Sin

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Next Post
Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.