• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Zumunci A Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Yake Da Danko Matuka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Zumunci A Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Yake Da Danko Matuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ta yanar gizo, shugaban kasar Equatorial Guinea, Mr. Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, wanda ya yi ziyarar aiki a birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, ya gana da wakilan malamai da dalibai na wata makarantar firamare da ke gundumar Jinping ta lardin Yunnan da ke kudu maso yammacin kasar Sin. 

To, amma ina dalilin ganawar? 

Ashe, a yayin ziyarar da shugaban ya kawo kasar Sin a watan Afrilun shekarar 2015, a madadin gwamnatin kasarsa ya sanar da samar da gudummawar kudi don a gyarawa, da fadada wata makarantar firamare da ke gundumar Jinping, don nuna godiya ga kasar Sin bisa yadda ta dade tana taimakawa kasarsa wajen tabbatar da bunkasuwa. Bayan shekara guda, an kammala gina wani gini mai bene biyar a makarantar, matakin da ya kyautata yanayin karatu ga yaran wurin. Don tunawa da dankon zumunci a tsakanin kasashen biyu kuma, an gyara sunan makarantar ya zama makarantar sada zumunta a tsakanin Sin da Equatorial Guinea. A cikin shekaru 9 da suka gabata, sama da yara 2000 sun kammala karatu a makarantar.

A hakika, kasar Equatorial Guinea kasa ce mai tasowa wadda ba ta da wadata, amma a yayin da ita kanta ke bukatar taimako, sai ga shi ta samar da gudummawa ga kasar Sin, kuma wannan ba shi ne karon farko na hakan ba, duba da cewa tun a shekarar 2008 a yayin da mummunar girgizar kasa ta afkawa kasar Sin, kasar ta Equatorial Guinea ta samar da gudummawar kudin EURO miliyan biyu ga kasar Sin.

Tabbas abu ne da ya ratsa zukatanmu, kuma ba a rasa irin wadannan labarai da suka faru a tsakanin Sin da kasashen Afirka. To, amma me ya sa Sin da kasashen Afirka suke da zumunci mai danko kamar haka? 

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Lallai kasancewar kasar Sin kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kuma Afirka nahiya ce mafi yawan kasashe masu tasowa, bangarorin biyu sun fuskanci makamantan abubuwan da suka faru gare su a tarihi, suna kuma da buri kusan iri daya da suke neman cimmawa, hakan ya sa dankon zumunci a tsakaninsu ya yi ta karfafa, kuma suke hada kai da juna don tabbatar da makomarsu ta bai daya. Idan ba a manta ba, a shekarun 1960 zuwa na 1970, Sinawa sama da dubu 50 sun hada kai da al’ummar Afirka wajen gina hanyar dogo ta Tanzania da Zambia, inda suka zubar da gumi da jini, har ma suka sadaukar da rayukansu, layin dogon da ya zama alamar zumunci a tsakaninsu. A shekarar 1971 kuma, kasashen Afirka sun bai wa kasar Sin babban taimako wajen mayar da ita kan kujerarta a MDD, inda daga cikin kasashe 23 da suka gabatar da shawarar, 11 sun kasance kasashen Afirka, baya ga kuri’u 76 da aka kada na nuna amincewa, wadanda a cikinsu wasu 26 kasashen Afirka ne suka kada. Yayin da aka shiga sabon karnin da muke ciki, huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ma sai karfafa take ta yi. A shekarar 2000, bangarorin biyu sun kafa dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC a takaice, dandalin da ya zamanto muhimmin tsari na yin shawarwari, da kuma hadin gwiwa a tsakanin su cikin shekaru 24 da suka gabata, tare da samar da nasarorin a zo a gani.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping yana dora matukar muhimmanci a kan cudanyar Sin da kasashen Afirka, wanda bayan da aka zabe shi a matsayin shugaban kasar a shekarar 2013, da kuma sake zabarsa a shekarar 2018, ya kai ziyararsa ta farko a matsayin shugaban kasa duk a nahiyar Afirka. Baya ga haka, ya kuma gabatar da manufar da ya kamata a bi wajen hulda da kasashen Afirka, wato nuna sahihanci, da samar da hakikanin sakamako, da kauna da kuma rikon gaskiya, don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakaninsu.

A jawabin da ya gabatar a yayin ziyararsa a kasar Tanzania a shekarar 2013, ya ce, “kasar Sin ta samar da gudummawa ga kasashen Afirka gwargwadon karfinta, kuma godiya take ga kasashen Afirka, da ma al’ummarsu bisa ga goyon baya da ma taimako da suka dade suna ba ta. A kan batutuwan da suka shafi babbar moriyar juna, kullum matsayinmu a bayyane yake, wato muna tsayawa tsayin daka wajen goyon bayan juna.” Furucinsa ya bayyana ainihin zumunci dake tsakanin sassan Afrika da Sin. (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaJihar XinjiangLi Qiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Batun Biyan Dubu ₦105 Mafi Ƙarancin Albashi Ƙanzon Kurege Ne – Fadar Shugaban Ƙasa

Next Post

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

1 hour ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

2 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

3 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

4 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

5 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

7 hours ago
Next Post
Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.